Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Jirgin Sama Mai Saukar Ungulu Ya Kashe Mutane Biyar A Tanzaniya
Published: December 25, 2025 at 8:27 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wani jirgin sama mai saukar ungulu ya fadi a kan dutsen Kilimanjaro na kasar Tanzaniya ya kashe mutane 5

Hukumar kula da gandun daji ta kasar ta ce wadanda suka mutu sun hada da dan jagora daya da wani likita, dukkansu ‘yan kasar ta Tanzaniya, sai kuma matukin jirgin dan kasar Zimbabwe da wasu mutane biyu ‘yan yawon shakatawa da bude ido ‘yan kasar Jamhuriyar Czech.

Jirgin na helkwafta ya fadi ne a kusa da wani sansani mai suna Barafu, inda masu hawa dutsen suke yada zango su huta kafin su ci gaba da kokarin hawa kololuwarsa.

Wata jarida mai suna Mwananchi da kuma gidan telebijin na “East Africa TV” sun ambaci jami’in ‘yan sanda na yankin yana fadin cewa jirgin ya je shi aikin kwaso marasa lafiya ne.

Dutsen na Kilimanjaro, wanda ya fi kowane dutse tudu a nahiyar Afirka, yayi kusan cika mita dubu 6 daga doron teku.

Wannan hatsari ya faru a tsakanin mita dubu 4 da 600 da kuma mita dubu 4 da 700.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: A Hudubar Kirsimeti Paparoma Leo Ya Jajantawa Al’ummar Falatsinu A Yankin Zirin Gaza
Next Post: Ukraine Tana Cigaba Da Tattaunawa Da Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri Afrika
Kasar Chadi Ta Rufe Iyakar Ta Da Kasar Sudan Afrika
Farashin Danyen Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Afrika
Gwamnan Jihar Gombe Ya Umurci A Rufe Makarantu Labarai
Ruwa Kamar Da Bakin Kwarya Ya Haifar Da Mutuwar Mutane A Nairobi Afrika
Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Gambiya Ta Gayawa Kotun MDD Shirin Myanmar Akan Musulmai Afrika
  • Ga Fili Ga Doki Najeriya
  • Bisa Alamu Hadinkan Kasashen Yankin Sahel Zai Haifar Da Nagarta Afrika
  • Masar Ta Jibge Jiragen Yaki Marasa Matuka Afrika
  • Za’a Jima Ana Fama Da Tsadar Farashin Mai Afrika
  • Iran Ta Kama Wasu ‘Yan Leken Asiri Afrika
  • Anyi Jana’izar Mahaifiyar Nasiru El Rufai A Abuja Afrika
  • Magoya Bayan Obi Sun Yi Tutsu Gabanin Zaben 2027 Siyasa
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.