Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Jirgin Sama Mai Saukar Ungulu Ya Kashe Mutane Biyar A Tanzaniya
Published: December 25, 2025 at 8:27 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wani jirgin sama mai saukar ungulu ya fadi a kan dutsen Kilimanjaro na kasar Tanzaniya ya kashe mutane 5

Hukumar kula da gandun daji ta kasar ta ce wadanda suka mutu sun hada da dan jagora daya da wani likita, dukkansu ‘yan kasar ta Tanzaniya, sai kuma matukin jirgin dan kasar Zimbabwe da wasu mutane biyu ‘yan yawon shakatawa da bude ido ‘yan kasar Jamhuriyar Czech.

Jirgin na helkwafta ya fadi ne a kusa da wani sansani mai suna Barafu, inda masu hawa dutsen suke yada zango su huta kafin su ci gaba da kokarin hawa kololuwarsa.

Wata jarida mai suna Mwananchi da kuma gidan telebijin na “East Africa TV” sun ambaci jami’in ‘yan sanda na yankin yana fadin cewa jirgin ya je shi aikin kwaso marasa lafiya ne.

Dutsen na Kilimanjaro, wanda ya fi kowane dutse tudu a nahiyar Afirka, yayi kusan cika mita dubu 6 daga doron teku.

Wannan hatsari ya faru a tsakanin mita dubu 4 da 600 da kuma mita dubu 4 da 700.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: A Hudubar Kirsimeti Paparoma Leo Ya Jajantawa Al’ummar Falatsinu A Yankin Zirin Gaza
Next Post: Ukraine Tana Cigaba Da Tattaunawa Da Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

Ambaliyar Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutum 13 A Malawi Labarai
Kasar China Tana Cigaba Da Nuna Fin Karfi Ga Kasar Taiwan Labarai
Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta Afrika
Sanata Sa’idu Alkali Ya Kaurace Wa Zaben Fidda Gwani Afrika
Masu Goyon Bayan Palasdinawa Sunyi Gangamin Zanga Zanga A Australia Labarai
Ministan Harkokin Wajen Rasha Dana Iran Sun Tattauna Don Kawo Karshen Yaki A Gabas Ta Tsakiya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Zata Fara Sayar Da Maganin Hana Kiba Da Jin Yunwa Amurka
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Daruruwan Mutane A Afirka Ta Kudu Afrika
  • Wani Abu Ya Fashe A Ofishin Jakadancin Amurka Dake Kasar Norway Afrika
  • Kwankwaso Yayi Kakkausar Lafazi Bayan Ficewar Abba Kabir Yusuf Daga NNPP Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Akwai Nasara A Tattaunawar Da Akeyi Tsakanin Iran Da Amurka Afrika
  • Afirka Ta Kudu Tace Bazata Yanke Alaka Da Iran Ba Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Rabawa Al’umma Tallafin Noma Afrika
  • Najeriya Da Maroko Sun Kulla Yarjejeniya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.