Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Jirgin Sama Mai Saukar Ungulu Ya Kashe Mutane Biyar A Tanzaniya
Published: December 25, 2025 at 8:27 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wani jirgin sama mai saukar ungulu ya fadi a kan dutsen Kilimanjaro na kasar Tanzaniya ya kashe mutane 5

Hukumar kula da gandun daji ta kasar ta ce wadanda suka mutu sun hada da dan jagora daya da wani likita, dukkansu ‘yan kasar ta Tanzaniya, sai kuma matukin jirgin dan kasar Zimbabwe da wasu mutane biyu ‘yan yawon shakatawa da bude ido ‘yan kasar Jamhuriyar Czech.

Jirgin na helkwafta ya fadi ne a kusa da wani sansani mai suna Barafu, inda masu hawa dutsen suke yada zango su huta kafin su ci gaba da kokarin hawa kololuwarsa.

Wata jarida mai suna Mwananchi da kuma gidan telebijin na “East Africa TV” sun ambaci jami’in ‘yan sanda na yankin yana fadin cewa jirgin ya je shi aikin kwaso marasa lafiya ne.

Dutsen na Kilimanjaro, wanda ya fi kowane dutse tudu a nahiyar Afirka, yayi kusan cika mita dubu 6 daga doron teku.

Wannan hatsari ya faru a tsakanin mita dubu 4 da 600 da kuma mita dubu 4 da 700.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: A Hudubar Kirsimeti Paparoma Leo Ya Jajantawa Al’ummar Falatsinu A Yankin Zirin Gaza
Next Post: Ukraine Tana Cigaba Da Tattaunawa Da Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

APC Ta Bayyana Abba Yusuf A Matsayin Halastaccen Ɗan Takara Bayan Cika Sharudda Afrika
Shugaba Trump Ya Bukaci A Cigaba Da Zanga Zanga A Iran Labarai
China Ta Dawo Da Harajin Magungunan Hana Haihuwa Labarai
Gwamnatin Jihar Neja Ta Soke Lasisin Mallakar Wasu Manyan Filaye A Jihar Labarai
Hukumar Zabe A Najeriya Ta Cigaba Da Rijistar Katin Zabe Labarai
Hukumar Upper Benue Zata Inganta Noma A Dadinkowa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Kai Shugaban Kasar Venezuela Kotu Amurka
  • Emmanuel Macron: Yakamata Wani Sashi Ya Rika Takawa Wani Sashi Birki A Tsarin Demokradiya Amurka Amurka
  • Sojin Israela Sunkai Hari Kan Falatsinawa Tsaro
  • Ukraine Zata Sayi Iskar Gas Daga Mozambique Afrika
  • ‘Yan Uwan Wadanda Aka Kashe Sunkai Kara Kotu Amurka
  • Gwamnatin Najeriya Ta Horar Da Matasa Sama 7,000 A Matsayin Masu Tsaron Daji Labarai
  • Akwai Yiwuwar Iran Da Amurka Su Cimma Matsayar Dakatar Da Shirin Nukiliya Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.