Wani jirgin sama mai saukar ungulu ya fadi a kan dutsen Kilimanjaro na kasar Tanzaniya ya kashe mutane 5
Hukumar kula da gandun daji ta kasar ta ce wadanda suka mutu sun hada da dan jagora daya da wani likita, dukkansu ‘yan kasar ta Tanzaniya, sai kuma matukin jirgin dan kasar Zimbabwe da wasu mutane biyu ‘yan yawon shakatawa da bude ido ‘yan kasar Jamhuriyar Czech.
Jirgin na helkwafta ya fadi ne a kusa da wani sansani mai suna Barafu, inda masu hawa dutsen suke yada zango su huta kafin su ci gaba da kokarin hawa kololuwarsa.
Wata jarida mai suna Mwananchi da kuma gidan telebijin na “East Africa TV” sun ambaci jami’in ‘yan sanda na yankin yana fadin cewa jirgin ya je shi aikin kwaso marasa lafiya ne.
Dutsen na Kilimanjaro, wanda ya fi kowane dutse tudu a nahiyar Afirka, yayi kusan cika mita dubu 6 daga doron teku.
Wannan hatsari ya faru a tsakanin mita dubu 4 da 600 da kuma mita dubu 4 da 700.


