Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Gwamnan Jihar Kano Ya Fice Daga Jam’iyar NNPP
Published: January 23, 2026 at 4:16 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP), yana mai danganta matakin da tsanantar rikice-rikicen cikin gida a jam’iyyar da kuma buƙatar kare muradun al’ummar jihar Kano gaba ɗaya.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Juma’a.

A cikin wasiƙar da ya aike wa Shugaban mazabar Diso-Chiranchi na jam’iyyar NNPP a Ƙaramar Hukumar Gwale, gwamnan ya sanar da janyewarsa daga jam’iyyar, wanda zai fara aiki daga ranar Juma’a, 23 ga Janairu, 2026.

“Ina rubuta wannan wasiƙa cikin matuƙar godiya domin sanar da shugabannin jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP) cewa na yanke shawarar ajiye kasancewata ɗan jam’iyyar, daga ranar Juma’a, 23 ga Janairu, 2026.”

Gwamna Yusuf ya bayyana godiyarsa ga jam’iyyar bisa damar da ta ba shi da kuma goyon bayan da ya samu tun farkon tafiyarsa ta siyasa a ƙarƙashin NNPP.

Ya kuma yi nuni da cewa jam’iyyar na fuskantar rikice-rikice na cikin gida da kuma ƙalubalen shari’a da suka daɗe suna dagula tsarinta a matakin ƙasa.

A cewarsa, rikice-rikicen sun haifar da rarrabuwar kawuna tare da raunana haɗin kan jam’iyyar.

Gwamnan ya ce ya ɗauki matakin ne bayan zurfin nazari, kuma bisa la’akari da muradun jama’a kawai.

Ya jaddada cewa ya ɗauki wannan mataki ne cikin kyakkyawar niyya ba tare da wata ƙiyayya ba.

“Na ɗauki wannan mataki cikin kyakkyawar niyya, ba tare da wata muguwar manufa ko ƙiyayya ba, tare da ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban jihar Kano.”

Gwamnan ya fice tare da mambobi 21 na Majalisar Dokokin jihar Kano, mambobi 8 na Majalisar Wakilai ta Tarayya, da kuma shugabannin ƙananan hukumomi 44 na Jihar Kano.

Sakataren jam’iyyar NNPP na Ward ɗin Diso-Chiranchi, Kabiru Zubairu, ya tabbatar da karɓar wasiƙar tare da yabawa gwamnan bisa ayyukan ci gaba da ya aiwatar a fannoni daban-daban.

Siyasa

Post navigation

Previous Post: Tsohon Lauyan Amurka Jack Smith Ya Fadi Maganganu Game Da Donald Trump
Next Post: Kasar Uganda Ta Tsare ‘Yan Jam’iyyun Adawa Dubu Biyu

Karin Labarai Masu Alaka

China Ta Kori Wakilan Majalisar Dokoki Uku A Kasar Labarai
Jagoran Kwankwasiya A Najeriya Ya Koma Jam’iyar ADC Labarai
INEC: Akwai Yiwuwar Dage Zaben 2027 Saboda Azumi Labarai
Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
Chadi Ta Sauyawa ‘Yan Gudun Hijira Matsuguni Afrika
INEC Mayar Da Lokacin Zaɓen 2027 Kafin Azumi Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Zamu Hana Wasu ‘Yan-Najeriya Visa Shiga Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Bayan Ya Ziyarci Kwankwaso Gawuna Zai Karbi Katin ADC Afrika
  • Yohanna YD Buru: Makon Haɗin Kan Addinai Ya Ƙarfafa Ilimin Zaman Lafiya A Najeriya Labarai
  • An Maka Wasu Jami’an Immigration A Kotu Bisa Zargin Rashin Da’a A Birtaniya Labarai
  • Fargaba Ta Karu Duk Da Tsagaita Wuta Tsakanin Iran Da Amurka Afrika
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Murkushe Wani Yunkurin Juyin Mulki A Jamhuriyar Benin Afrika
  • Masarautar Borgu a Jihar Neja na neman daukin Gwamnatin Najeriya akan matsalar rashin tsaro Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.