Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Karamar Sallah: Hukumar Kashe Gobara A Gombe Ta Kuduri Aniyar Kare Al’umma
Published: March 19, 2026 at 2:11 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: March 19, 2026

Karamar Sallah: Hukumar Kashe Gobara Ta kasa Reshen Jihar Gombe, Ta Fidda Jawabai Domin Kare Lafiyar Al’umma.

Shugaban Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya reshen jihar Gombe, DCF Suleiman Mohammed Suleiman, ya taya al’ummar Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan, tare da kira ga mazauna jihar da su gudanar da bukukuwan Sallah cikin kulawa da tsaro.

Kwarewa ta nuna cewa a lokutan bukukuwa ana yawan samun aukuwar gobara da wasu hatsarori da za a iya kaucewa, sakamakon karuwar ayyuka a gida da kasuwanci. Saboda haka, Hukumar na kira ga jama’a da su dauki matakan kariya a kowane lokaci.

Ana shawartar mazauna da su kula da yadda suke sarrafa silinda na gas da kayan lantarki, su guji barin girki ba tare da kulawa ba, sannan su nisanci lodin wutar lantarki fiye da kima. Haka kuma, dole ne a rika amfani da janareto a waje mai isasshen iska, yayin da ake bukatar a adana abubuwa masu kamawa da wuta a wurare masu aminci, nesa da zafi.

A lokacin taruka, ana bukatar kulawa da yara, samar da isasshen iska, da kuma kiyaye doka da oda. Haka kuma, a guji yin ajiye motoci ba bisa ka’ida ba wanda zai iya hana motocin agaji wucewa.

Dangane da yanayin zafi da ake ciki a halin yanzu, ana kara jaddada wa jama’a da su rika shan ruwa sosai, su rage kasancewa cikin tsananin zafi, tare da lura da alamomin cututtukan da ke da nasaba da zafi.

Hukumar ta kuma ja hankalin jama’a kan hadarin da ke tattare da rashin kula wajen sarrafawa da adana man fetur. Don haka ana kira ga kowa da kowa da ya yi taka-tsantsan musamman a gidaje da kuma wuraren sayar da mai.

Idan wata gobara ko wani hatsari ya faru, yana da matukar muhimmanci a kai rahoto cikin gaggawa ta wadannan lambobi: Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya, Reshen Jihar Gombe: 070-314-97455

Lambar Gaggawa ta Kasa: 112

Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya reshen Jihar Gombe na nan a shirye domin daukar mataki a kowane lokaci, tare da jaddada cewa kare lafiyar jama’a alhaki ne na kowa da kowa.

Afrika, Kimiya, Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: An Gudanar Da Idin Karamar Sallah A Birnin Niamey
Next Post: Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Jama’ar Arewa Maso Gabas

Karin Labarai Masu Alaka

Samar Da Albarkatun Mai Ya Ragu A Iraq Afrika
Hukumar EFCC Ta Kama Dan Kasuwa A Kamaru Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
Isra’ila Ta Kashe Babban Jami’in Tsaron Iran Ali Larjani Afrika
Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe Afrika
Kungiyar Kiristoci Ta Wanke Gwamnan Bauchi Daga Zargin Ta’addanci Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Rikici Ya Barke A Kano Bayan Kashe Wani Matashi Da Ake Zargi Da Kashe Ladani Najeriya
  • INEC Mayar Da Lokacin Zaɓen 2027 Kafin Azumi Najeriya
  • Babban Sufeton ‘Yan Sandan Najeriya Ya Sauka A Mukaminsa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hikima Da Jagorancin Sarkin Gombe A Shekaru 12 Na Jagoranci Afrika
  • Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Kashe-kashen Jos Da Kaduna Afrika
  • Jirgin Sama Mai Saukar Ungulu Ya Kashe Mutane Biyar A Tanzaniya Afrika
  • Gwamnatin Jihar Neja Ta Soke Lasisin Mallakar Wasu Manyan Filaye A Jihar Labarai
  • Gwamnatin Najeriya Zata Rabawa Al’umma Tallafin Noma Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.