Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gidauniya: An Fara Tiyatar ‘Hernia’ Da ‘Hydrocele’ Kyauta A Jihar Katsina
Published: December 13, 2025 at 10:29 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 13, 2025

Gidauniyar Alhaji Dahiru Barau Mangal, wato Mangal Foundation, ta fara gudanar da tiyatar cutar Hernia da Hydrocele kyauta ga mutane sama da 800 a jihar Katsina.

An fara aikin ne a Babban Asibitin Katsina ranar Juma’a 12 ga Disamba, 2025, bayan kammala tantance mutanen da ke fama da cututtukan a kwanakin baya.

A yayin tantancewar, an gano mutane da dama da ke bukatar tiyata, inda gidauniyar ta dauki nauyin aikin kyauta, ba tare da wadanda suka amfana sun biya ko sisi ba.

Da yake jawabi yayin fara aikin, ɗaya daga cikin ‘yan kwamitin amintattu na gidauniyar, Alhaji Hussaini Kabir, ya bayyana cewa za a ci gaba da gudanar da tiyatar har zuwa ranar Lahadi.

Alhaji Hussaini Kabir ya kara da cewa, bayan an yi wa marasa lafiya aikin, gidauniyar za ta ci gaba da daukar nauyin kulawa da su da magunguna har zuwa lokacin da za a sallame su daga asibiti.

Ya bayyana cewa, a lokacin tantancewar, an duba daruruwan mutane masu fama da matsalolin lafiya daban-daban, inda da yawa daga cikinsu aka ba su magunguna kyauta aka kuma sallame su.

Alhaji Kabir ya jaddada cewa wannan ba shi ne karo na farko da gidauniyar ke gudanar da irin wannan aiki ba, yana mai cewa a duk shekara ana shirya irin wannan aiki domin tallafawa al’umma.

Wasu daga cikin wadanda suka amfana da shirin sun bayyana godiya da addu’o’i ga shugaban gidauniyar, bisa wannan tallafi.

Sun kuma yi kira ga gwamnatoci, kamfanoni da masu hannu da shuni da su yi koyi da gidauniyar wajen tallafa wa marasa galihu a fadin kasar.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Amurka Ta Daina Bawa Israila Bayanan Sirri
Next Post: Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano

Karin Labarai Masu Alaka

Tawagar IMF Tana Kasar Kenya Domin Tattauna Bada Lamuni Labarai
Gwamnatin Amurka Na Kokarin Watsi Da Tsohuwar Dokar Jones Labarai
Iran Tace Farisa Zata Kai Hari Kan Mayakan Amurka Amurka
Mun Kwato Kimanin Naira Biliyan 40 Na Badakala A Tsawon Shekara Daya Labarai
Fafaroma Leo Zai Ziyarci Kasashen Afirka Amurka
Shugabannin Darikar Anglican Sun Bada Sanarwar Kafa Sabuwar Majalisa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi
  • Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran
  • Iran Zata Mayarwa Amurka Martanin Harin Kharg
  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kungiyar Mata Manoma A Najeriya Ta Raba Kyautar Abinci A Gombe Afrika
  • Tinubu Yafara Wasu Dabaru Domin Samun Kuri’u Siyasa
  • FIFA Ta Yi Wa Malaysia Kaca-kaca Wasanni
  • Tinubu: Munsayi Jiragen Yaki Daga Wajen Amurka Amurka
  • ‘Yan Sandan Birnin New York Sun Karyata Zargin Jefa Bom Ga Masu Zanga Zanga Amurka
  • Shirin Kwace Iyakar Greenland Da Shugaba Trump Yakeyi Yabawa Kasashen Turai Mamaki Amurka
  • Shugaba Donald Trump Ya Bayyana Cewa Yana Cikin Masu Zaben Sabon Jagoran Iran Amurka
  • Cutar Zazzabin Lassa Tayi Ajalin Mutum 1 Yayinda Mutane 11 Suka Kamu A Jihar Gombe Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.