Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Gidauniya: An Fara Tiyatar ‘Hernia’ Da ‘Hydrocele’ Kyauta A Jihar Katsina
Published: December 13, 2025 at 10:29 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 13, 2025

Gidauniyar Alhaji Dahiru Barau Mangal, wato Mangal Foundation, ta fara gudanar da tiyatar cutar Hernia da Hydrocele kyauta ga mutane sama da 800 a jihar Katsina.

An fara aikin ne a Babban Asibitin Katsina ranar Juma’a 12 ga Disamba, 2025, bayan kammala tantance mutanen da ke fama da cututtukan a kwanakin baya.

A yayin tantancewar, an gano mutane da dama da ke bukatar tiyata, inda gidauniyar ta dauki nauyin aikin kyauta, ba tare da wadanda suka amfana sun biya ko sisi ba.

Da yake jawabi yayin fara aikin, ɗaya daga cikin ‘yan kwamitin amintattu na gidauniyar, Alhaji Hussaini Kabir, ya bayyana cewa za a ci gaba da gudanar da tiyatar har zuwa ranar Lahadi.

Alhaji Hussaini Kabir ya kara da cewa, bayan an yi wa marasa lafiya aikin, gidauniyar za ta ci gaba da daukar nauyin kulawa da su da magunguna har zuwa lokacin da za a sallame su daga asibiti.

Ya bayyana cewa, a lokacin tantancewar, an duba daruruwan mutane masu fama da matsalolin lafiya daban-daban, inda da yawa daga cikinsu aka ba su magunguna kyauta aka kuma sallame su.

Alhaji Kabir ya jaddada cewa wannan ba shi ne karo na farko da gidauniyar ke gudanar da irin wannan aiki ba, yana mai cewa a duk shekara ana shirya irin wannan aiki domin tallafawa al’umma.

Wasu daga cikin wadanda suka amfana da shirin sun bayyana godiya da addu’o’i ga shugaban gidauniyar, bisa wannan tallafi.

Sun kuma yi kira ga gwamnatoci, kamfanoni da masu hannu da shuni da su yi koyi da gidauniyar wajen tallafa wa marasa galihu a fadin kasar.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Amurka Ta Daina Bawa Israila Bayanan Sirri
Next Post: Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano

Karin Labarai Masu Alaka

Sabuwar Shekarar Musulunci 1448: Kiristoci Sun Yi Murna, Sunyi Kiran Samar Da Hutu Ga Shekarar Musulunci Afrika
Amurka Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashe Hudu Domin Inganta Kiwon Lafiya Labarai
Babban Sakataren MDD Yayi Allah Wadai Da Matakin Soja A Gabas Ta Tsakiya Afrika
Gwamnatin Tinubu Ta Karyata Kafa Kamfanin Gwal A Legas Labarai
Asusun IMF Ya Bukaci Afirka Ta Kudu Ta Rage Bashin Da Suke Karba Afrika
Shugaban Amurka Donald Trump Yace Amurka Zata Kai Babban Farmaki Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jami’an tsaro sama da dubu biyar ne zasuyi aikin tabbatar da tsaro Alokacin bikin karamar sallah a Jihar Nejan Najeriya. Najeriya
  • Shirin Kwace Iyakar Greenland Da Shugaba Trump Yakeyi Yabawa Kasashen Turai Mamaki Amurka
  • Bahrain Ta Gabatar Da Kudurin Sulhu Ga MDD Afrika
  • Gwamnatin Sham Tace Harin Kurdawa Ya Hallaka Sojojin Kasar Afrika
  • Amy Hunt Ta Zama Sabuwar Tauraruwar Wasannin Guje-guje Ta Birtaniya Wasanni
  • Mutane Biyu Sun Rasa Rayukansu A Hatsarin Da Ya Rutsa Da Antothy Joshua Najeriya
  • Rahoton MDD Yace An Kashe Fiye Da Farar 1000 A Sudan Labarai
  • Mayakan M23 Sun Tsagaita Wuta A Gabashin Kwango Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.