Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Hare Hare Daban Daban A Najeriya
Published: February 5, 2026 at 7:33 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

‘Yan bindiga sun kashe mutane kimanin 100 a wasu hare-haren da suka kai kan wasu kauyuka biyu a yankunan tsakiya da kuma arewacin Najeriya, yayin da jami’an tsaro ke ci gaba da neman mutanen da suka kubuta da rayuka suke kuma farautar ‘yan bindigar.

A jihar Kwara dake yankin tsakiyar Najeriya, ‘yan bindiga sun kai farmaki a wani kauye mai suna Woro, inda suka kashe mutane masu yawa.

Gwamnan jihar ta Kwara, Abdulrazaq Abdulrahman, wanda ya ziyarci inda abin ya faru ranar laraba tare da wasu kwamandojin soja da sojoji kimanin dubu 1, ya fadawa wani dan jarida dake zaune a Amurka, Farooq Kperogi, cewar sun tabbatar da mutuwar mutane 75 ya zuwa lokacin da suka yi magana, amma kuma adadin yana iya karuwa yayin da ake ci gaba da neman mutanen da suka bace.

Tun da farko, wani dan majalisa mai wakiltar yankin ya fadawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa mutane har 170 suka mutu.

Shi ma kwamandan birged ta 22 ta dakarun Najeriya dake Ilorin, Birgediya Janar Nicholas Rume, ya fadawa Malam Farooq Kperogi cewa sun shawo kan lamarin a yanzu.

Wannan shine hari mafi muni da aka gani cikin shekarar nan a wannan yanki mai iyaka da jihar Neja, inda ake fama da hare-haren ‘yan bindiga masu kai farmaki a kan kauyuka da satar jama’a don yin garkuwa da su tare da satar dabbobi.

Dan majalisar da yayi magana da kamfanin dillancin labaran Reuters ta waya, Saidu Baba Ahmed, yace ‘yan bindigar sun tattara mutanen garin, suka daddaure hannayensu ta baya, sannan suka kashe su. Haka kuma ‘yan bindigar sun cinna wuta a gidaje da shaguna.

A wani harin na daban kuma, ‘yan bindiga sun kashe mutane akalla 21 a jihar Katsina dake arewacin Najeriya, inda ‘yan sanda da mazauna garin suka ce wadannan mahara sun bi gida-gida suna harbe mutane.

Wannan harin ya kawo karshen sulhun da aka yi a tsakanin mutanen wannan gari da ‘yan bindigar watanni 6 da suka shige.

Wannan hari na jihar Katsina ya nuna irin halin kaka-ni-ka-yin da mutane suke ciki a yankunan karkara na arewacin Najeriya, wadanda suka nemi yin sulhu da ‘yan bindigar da suke addabar su.

Mazauna irin wadannan kauyuka a akasarin lokuta suna harhada kudade da abinci domin bawa wadannan ‘yan bindiga da nufin neman su kyale su.

Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai
Next Post: Amurka Da Iran Zasu Tattauna A Kasar Oman

Karin Labarai Masu Alaka

Taron Masu Mu’amala Da Kafar Facebook A Kano Afrika
Papa Roma Leo Yace Zai Cigaba Da Sukan Yake Yake Afrika
Wasu Mayakan ‘Yan Tawaye Sunkai Hari Filin Jirgin Saman Kasar Kwango Labarai
Kasar Saudiya Zatayi Gwajin Noman Dabino A Kano Labarai
Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala Afrika
Rahoton Leken Asiri Yanuna Cewa Harin Amurka Bazai Samar Da Shugabanci A Iran Ba Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Da Haɗin Guiwar Gwamnatin Jihar Zamfara Suna Shirin Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Jihar Rumbun Hotuna
  • Zanga-Zangar Adawa Da Harin Amurka Da Isra’ila Ya Zamo Tarzoma A Pakistani Afrika
  • Amurka Ta Kama Wani Jirgin Dakon Mai Amurka
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
  • An Kaddamar Da Kwamitin Kwallon Kafa A Tsakanin Masarautun Jihar Gombe Labarai
  • Majalisar Wakilai Tayi Allah Wadai Da Hare-Haren ‘Yan Bindiga A Gombe Labarai
  • Onana Ba Ya Cikin Tawagar Kamaru (AFCON) Wasanni
  • Sojojin Faransa Sun Karyata Zargin Bobi Wine Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.