Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Amurka Da Iran Zasu Tattauna A Kasar Oman
Published: February 5, 2026 at 7:46 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Amurka da Iran sun yarda zasu tattauna gobe Jumma’a a kasar Oman, a cewar jami’an kasashen biyu, sai dai kuma har yanzu ba su cimma daidaituwa a kan nacewar da Amurka take yi cewa lallai tattaunawar ta hada har da makamai masu linzami na Iran, yayin da ita kuma take cewa shirinta na nukiliya kawai zata tattauna akai.

Wannan yunkurin na diflomasiyya yana zuwa a yayin da Amurka take ta girka sojoji a yankin gabas ta tsakiya, su kuma kasashen yankin suke kokarin ganin an kaucewa fadan soja da suke fargabar cewa zai iya yaduwa zuwa fadin yankin.

Sabanin ra’ayi a game da abubuwan da za a tattauna a kai sun janyo tababa a kan ko za a iya yin zaman, abinda zai haifar da yanayin da shugaba Donald Trump na Amurka zai iya yin amfani da shi don aiwatar da barazanarsa ta kai hari a kan Iran.

Jami’an Amurka da na Iran sun ce sassan biyu sun yarda za a gudanar da wannan taron a Muscat, babban birnin Oman, a bayan da tun farko aka ce za a yi ne a Istanbul na Turkiyya.

Amma babu wata alamar dake nuna cewa sun cimma daidaituwa a kan ajandar wannan taron.

Amurka, Labarai

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Hare Hare Daban Daban A Najeriya
Next Post: Kasar Amurka Da Rasha Zasu Kawo Karshen Tsagaita Nukiliya

Karin Labarai Masu Alaka

Jami’an Shiga Da Fice A Afirka Ta Kudu Sun Tafka Badakalar Kudade Afrika
Meyasa Israela Take Hana Kaiwa Gaza Kayan Tallafi Afrika
“Yan Wasan Super Eagles Sun Karbi Alkawarin Da Gwamnati Tayi Musu AFCON 2023 Labarai
Bankin Duniya Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Afirka Da Yankin Sahara Afrika
Kasar China Ta Sauka Daga Ragamar Bada Bashi Labarai
Sojoji Zasu Taimakawa ‘Yan Sanda Wajen Yaki Da Mugayen Ayyuka Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dakarun Tsaron Ruwan Amurka Sunfara Killace Hanyoyi Amurka
  • CAF Ta Fara Binciken Rikicin Bayan Wasa Tsakanin Algeria Da Najeriya Wasanni
  • Netanyahu Ya Umarci Rundunar Sojoji Takara Fadada Ayyukanta A Lebanon Afrika
  • An Sako Dan Siyasar Kasar Venezuela Daga Gidan Yari Labarai
  • Kungiyar ISIS Ta Kashe Sojojin Amurka Biyu Amurka
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Umurci Janyewa Manyan Mutane ‘Yan Sanda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.