A ci gaba da yaki tsakanin Amurka, Isra’ila da Iran. Prime ministan Isra’ila, Benjamin Netanyaho, yace a jiya Laraba Iran bata da damar da zata wadatar da uranium ko kuma ta kera makamai masu linzami ba, abubuwan da gwamnatin Donald Trump tayi ikirari dasu wajen far wa Iran da yaki. Netanyaho ya kara da cewa Isra’ila zata tsagaita kai hare-hare nan gaba ga cibiyar gas na Iran kamar yadda shugaban Amurka Donlad Trump ya bukata.
Ma’aikatar tsaron Amurka ta Pentagon kuma na bukatar karin dala miliyan dubu dari biyu don gudanar da yaki da Iran, a cewar wani babban jami’i ya ce wannan kudade ne masu yawa ainun, kuma bayan karin kudaden da ma’aikatar tsaron ta samu a shekarar da ta gabata yayin dokar yanke haraji ta Trump.
Kasashen Canada, Faransa, Jamus Italy, Netherlands, Japan da Birtaniya sun yi Allah wadai da Harin da Iran ta kai kan jiragen ruwa da cibiyoyin makamashi da kuma ci gaba da rufe mashigin ruwa na Hormuz.
Wannan na zuwa ne bayan da Iran din ta mai da martani kan harin da Isra’ila ta kai kan cibiyar gas din ta.


