Wani hari daga Jirgi mara matuki na drone daga kasar Sudan ya hallaka mutane 17 a kasar Chadi, ciki har da wasu dake halartar zaman makoki, a cewar gwamnatin Chadi da kuma mazauna wajen a ranar Alhamis. Shugaban kasar Chadi ya dau alwashin daukan fansa idan aka sake kawo musu wani harin.
Harin ya fada ne kan garin Tine dake da iyaka da kasar Sudan a ranar Laraba da rana yayin da mutane suka taru suna zaman makoki da gudanar da addu’o’i a wani gida.
Abubuwa biyu ne suka yi bindiga a cewar wani mazaunin wurin, kuma wasu daga cikin mutanen dake zaman makokin sun rasa rayukan su tare da yara dake wasa kusa da wajen.
Hukumomi a garin sun ce ba’a tantance wa ke da alhakin kai harin ba.


