Hukumar kula da makamashin nukiliya ta Duniya, (wato IAEA), ta gabatar da wani rahoto na sirri, inda ta bukaci Iran da ta barta ta duba duk Wasu wuraren ta na nukiliya, inda tayi nuni da cibiya ta Isfahan, a matsayin wurin da take da bukatar dubawa, domin makamashin Uranium da kusan za’a iya yin bomb da shi dake ajiye a nan.
An aikewa da mambobin hukumar IAEA 35 rahoton, kafin zaman ganawa na bayan watanni 3 da suke yi, wanda za’a yi mako mai zuwa, ana tsaka da tattaunawa tsakanin Amurka da Iran, wadda tattaunawar da aka yi ranar Alhamis bata cimma wata matsaya ba.
A watan Yunin bara ne Amurka da Isra’il suka kai harin bomb a sansanonin nukilya na Iran, kuma tun a lokacin Iran taki ta nuna abinda ya faru ga ma’adanin ta na Uranium, ko ta bar jami’an IAEA su je su duba wuraren.


