Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya
Published: June 18, 2026 at 7:23 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Sarkin Jaurowal dake Masarautar Pindiga, Karamar Hukumar Akko ta Jihar Gombe, Comrade Ambassador Ibrahim Mu’azu Hassan, ya roƙi gwamnatoci a dukkan matakai su samar da muhimman kayan more rayuwa ga al’ummar da ke ƙarƙashinsa.

Yayin da yake Tattaunawa da Wakilin Amurka Ke Magana a jihar Gombe, sarkin ya roƙi shugabannin siyasa, masu hannu da shuni, da kuma ƙungiyoyi masu zaman kansu su tallafawa yankin ta hanyar sauƙaƙa samar da Hanyoyi, Cibiyoyin lafiya, da Makarantun ilimi.

Mu’azu Hassan ya bayyana damuwarsa kan halin da ababen more rayuwa ke ciki a yankin, musamman hanyoyi, wanda ya ce ya haddasa mutuwar akalla mata 5 da ba su samu damar samun magani a kan lokaci ba yayin da ake ɗaukarsu zuwa asibiti.

Ya yi kira ga gwamnatin Gwamna Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, Sanata Danjuma Goje mai wakiltar Gombe ta Tsakiya, da Dr. Usman Bello Kumo ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Akko, Alhaji Abubakar Abdullahi Mai Wanka dan majalisa mai wakiltar Akko ta Yamma dasu shiga tsakani su magance matsalolin da al’ummar yankin ke fuskanta.

Sarkin ya kuma yi ƙorafi kan watsar da aikin gina Makarantar Junior Secondary School ta Jaurowal da aka shirya yinta kuma basuyi ba har yau, inda ya ce ginin ya tsaya shekaru 7 da suka wuce, ya kuma ƙara da cewa mazauna yankin suna fama da matsaloli wajen samun ingantaccen ilimi da lafiya.

Ya kara roƙon gwamnati ta ba yankin kulawa, ta kuma ƙirƙiri “Ward” saboda Jaurowal yana da kauyuka kusan 10, ciki har da Garin Jauro Jibir, Labarfito, Dongoru Karama, Felawa, Bakkiti, Pali, Lafiyawo, da Ardowu,Garin Yabano etc.

Duk da yawan jama’a da gudummawar da suke bayarwa ga karamar hukumar, ya ce al’ummar yankin ba su ci moriyar ayyukan ci gaba da ‘ya’yan dimokuraɗiyya ba har yanzu.

Mu’azu Hassan ya roƙi hukumomi masu dacewa su ba da fifiko ga bukatun yankin, su inganta rayuwar mazauna yankin ta hanyar samar da ababen more rayuwa da ayyukan cigaban al’umma.

A karshe yana addu’a ga kasar Pindiga Emirates da Garin Jaurowal jihar Gombe da Nigerian baki daya da Allah yabasu zaman lfy da cigaba mai dorewa.

Afrika, Kiwon Lafiya, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Dakarun Sojin Najeriya Sun Kashe Yan Kungiyar Lakurawa
Next Post: Makokin Ashura: An Gudanar Da Taron Tunawa Da Aliyul Asghar A Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Ukraine Zata Sayi Iskar Gas Daga Mozambique Afrika
Shugaban Kasar Iran Yace Kasar Bata Da Kiyayya Tsakaninta Da Amurkawa Afrika
Kasar Jamus Ta Haramtawa Yara Kasa Da Shekaru 14 Hawa Dandalin Sada Zumunta Labarai
Rundunar Sojin Najeriya Ta Dakile Harin ‘Yan Ta’adda A Jihar Borno Labarai
Tinubu Ya Jaddada Buƙatar Kare Rayukan ‘Yan Afirka A Taron ECOWAS Afrika
Kawayen Amurka Bazasu Shiga Matakin Shugaba Trump Ba Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Ghana Ta Umarci ‘Yan Kasar Su Daina Zuba Jari A Kasashen Waje Afrika
  • Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya Amurka
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
  • Rikici Ya Lafa A Kasar Iran Bayan Daukar Matakai Labarai
  • Sojojin Amurka Sun Isa Najeriya Don Yaki Da Ta’addanci Amurka
  • Hukumar Hasashen Kasuwanci Na Zargin Saida Bayanan Sirri Amurka
  • Sojojin Najeriya Sun Kwato Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
  • Dottin Shara Ya Damu Jama’ar Havana Kasar Cuba Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.