Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Tinubu Ya Jaddada Buƙatar Kare Rayukan ‘Yan Afirka A Taron ECOWAS
Published: July 21, 2026 at 10:52 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi kira ga Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) da ta ɗauki tsauraran matakai kan ci gaba da hare-haren ƙyamar baƙi da ake kai wa ‘yan Najeriya da sauran ‘yan Afirka a ƙasar Afirka ta Kudu.

Tinubu ya bayyana hakan ne ta bakin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, yayin taron shugabannin ECOWAS karo na 69 da aka gudanar a birnin Freetown na ƙasar Saliyo.

Ya ce ya zama dole ECOWAS ta gabatar da batun a gaban Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU), domin a ɗauki matakin gaggawa kan hare-haren da ke barazana ga rayuka da dukiyoyin ‘yan Afirka.

Shugaban ya ce gwamnatin Najeriya ta yi Allah wadai da hare-haren, tana mai bayyana cewa ci gaba da yin shiru ta fuskar diflomasiyya kan irin waɗannan abubuwa na iya ƙarfafa masu aikata su.

A cewarsa, gwamnatin tarayya ta kwashe sama da ‘yan Najeriya 1,490 daga Afirka ta Kudu ta hanyar jigilar jirage bakwai domin kare rayukansu sakamakon rikice-rikicen.

Rahotanni sun nuna cewa Najeriya na tattaunawa da Ghana domin haɗa kai wajen matsa wa Tarayyar Afirka lamba ta ɗauki matakin hukunta Afirka ta Kudu kan ci gaba da hare-haren ƙyamar baƙi.

An bayyana cewa hare-haren ba ‘yan Najeriya kaɗai suka shafa ba, har ma da dubban ‘yan wasu ƙasashen Afirka da ke zaune da aiki a Afirka ta Kudu.

A wani ɓangaren kuma, Shugaba Tinubu ya sake jaddada aniyar Najeriya na goyon bayan shirin ECOWAS Compact for the Future of Regional Integration, wanda ke da nufin ƙarfafa haɗin kan ƙasashen yankin, inganta shugabanci nagari, bunƙasa kasuwanci tsakanin ƙasashe, da samar da kasuwar hada-hadar yanar gizo guda ɗaya domin faɗaɗa damar ayyukan yi ga matasa.

Ya ce tabbatar da shugabanci nagari da kare rayuka da haƙƙin ‘yan Afirka su ne manyan ginshiƙan samar da zaman lafiya da ci gaban nahiyar.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sana'o'i, Sauran Duniya, Siyasa, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Shari’ar Ta’addanci: Manyan Jagororin Ansaru Biyu Sun Amsa Laifi A Abuja
Next Post: Majalisar Dokokin Filato Ta Kare Kudirin Alawus Ga Tsofaffin ‘Yan Majalisa

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Haramta Sana’ar Bola Jari Tsaro
Fafaroma Leo Yayi Allah Wadai Bisa Karuwar Yake Yaken Gabas Ta Tsakiya Amurka
Tattaunawar Nukiliya Tsakanin Iran Da Amurka Yana Tasirin Akan Farashin Albarkatun Mai Amurka
Ga Fili Ga Doki Dambarwar APC Da ADC Najeriya
Kasashen Cambvodia Da Thailand Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Tsaro
Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Akwai Shakku Akan Sanin Wacce Kungiyar Kwallon Kaface Zata Lashe Gasar Kofin Afirka Da Akeyi A Morocco Nishadi
  • Najeriya Tayi Asarar Kusan Naira Triliyan 1 Sakamakon Harajin Trump Amurka
  • An Kashe Mutane 169 A Wani Harin Sudan Ta Kudu Afrika
  • An Bude Kamfanin Sarrafa Ma’adanai A Kasar Mozambique Labarai
  • An Kai Shugaban Kasar Venezuela Kotu Amurka
  • Anyi Girgizar Kasa Mai Karfi A Kasar Mexico Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Gurfaranar Da Wadanda Ake Zargi Takai Hari Gaban Kotu Najeriya
  • Shugaban Koriya Ta Arewa Ya Gabatar Da Gwajin Makami Mai Linzami Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.