Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Tinubu Ya Jaddada Buƙatar Kare Rayukan ‘Yan Afirka A Taron ECOWAS
Published: July 21, 2026 at 10:52 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi kira ga Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) da ta ɗauki tsauraran matakai kan ci gaba da hare-haren ƙyamar baƙi da ake kai wa ‘yan Najeriya da sauran ‘yan Afirka a ƙasar Afirka ta Kudu.

Tinubu ya bayyana hakan ne ta bakin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, yayin taron shugabannin ECOWAS karo na 69 da aka gudanar a birnin Freetown na ƙasar Saliyo.

Ya ce ya zama dole ECOWAS ta gabatar da batun a gaban Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU), domin a ɗauki matakin gaggawa kan hare-haren da ke barazana ga rayuka da dukiyoyin ‘yan Afirka.

Shugaban ya ce gwamnatin Najeriya ta yi Allah wadai da hare-haren, tana mai bayyana cewa ci gaba da yin shiru ta fuskar diflomasiyya kan irin waɗannan abubuwa na iya ƙarfafa masu aikata su.

A cewarsa, gwamnatin tarayya ta kwashe sama da ‘yan Najeriya 1,490 daga Afirka ta Kudu ta hanyar jigilar jirage bakwai domin kare rayukansu sakamakon rikice-rikicen.

Rahotanni sun nuna cewa Najeriya na tattaunawa da Ghana domin haɗa kai wajen matsa wa Tarayyar Afirka lamba ta ɗauki matakin hukunta Afirka ta Kudu kan ci gaba da hare-haren ƙyamar baƙi.

An bayyana cewa hare-haren ba ‘yan Najeriya kaɗai suka shafa ba, har ma da dubban ‘yan wasu ƙasashen Afirka da ke zaune da aiki a Afirka ta Kudu.

A wani ɓangaren kuma, Shugaba Tinubu ya sake jaddada aniyar Najeriya na goyon bayan shirin ECOWAS Compact for the Future of Regional Integration, wanda ke da nufin ƙarfafa haɗin kan ƙasashen yankin, inganta shugabanci nagari, bunƙasa kasuwanci tsakanin ƙasashe, da samar da kasuwar hada-hadar yanar gizo guda ɗaya domin faɗaɗa damar ayyukan yi ga matasa.

Ya ce tabbatar da shugabanci nagari da kare rayuka da haƙƙin ‘yan Afirka su ne manyan ginshiƙan samar da zaman lafiya da ci gaban nahiyar.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sana'o'i, Sauran Duniya, Siyasa, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Shari’ar Ta’addanci: Manyan Jagororin Ansaru Biyu Sun Amsa Laifi A Abuja
Next Post: Majalisar Dokokin Filato Ta Kare Kudirin Alawus Ga Tsofaffin ‘Yan Majalisa

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Habasha Ta Cimma Matsaya Da Masu Binta Bashi Afrika
Tsohon Jagoran Masu Kishin Kasa A Hungry Ya Amince Da Shan Kaye Labarai
Gwamnatin Najeriya Tace A Maboyar ‘Yan Ta’adda Aka Kai Harin Jilli Afrika
Hamas Ta Kwance Damara Afrika
Jihar Borno Ce Tayi Nasara A Gasan Karatun Al Qur’ani Na Kasa Najeriya
Majalisar Dokokin Kamaru Ta Amince Da Wasu Sauye Sauye Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Man Da Matatar Dangote Take Fitarwa Zuwa Kasashen Afirka Ya Karu Afrika
  • Ministocin Kasar Asia Zasu Gudanar Da Taro A Kasar Malaysia Tsaro
  • Kasar Sham Ta Sanar Da Tsagaita Wuta Tsakaninta Da Kungiyar Kurdawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • EU Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Amurka Da Iran Afrika
  • Hukumar EFCC Ta Kama Dan Kasuwa A Kamaru Afrika
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hukumar DSS Ta Sake Kama Abubakar Malami Labarai
  • Majalisar Dokokin Filato Ta Kare Kudirin Alawus Ga Tsofaffin ‘Yan Majalisa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.