Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Najeriya Da Dubai Zasu Karbi Bakoncin Taron Zuba Hannayen Jari
Published: January 13, 2026 at 4:58 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 13, 2026

Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya sanar da cewa Najeriya za ta karɓi bakuncin taron Investopia tare da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE) a birnin Legas a watan Fabrairu mai zuwa, domin jawo hankalin masu zuba jari daga sassa daban-daban na duniya.

Shugaban ƙasar ya bayyana hakan ne a yayin taron Abu Dhabi Sustainability Week (ADSW) na shekarar 2026, inda ya ce shirin zai taimaka wajen bunƙasa jarin da zai tallafa wa ci gaban tattalin arziki mai dorewa.

A gefen taron, Najeriya da UAE sun kuma rattaba hannu kan yarjejeniyar tattalin arziki ta CEPA, wadda ke da nufin zurfafa haɗin gwiwa a fannonin kasuwanci, makamashi, gine-gine, sufurin kayayyaki da kasuwancin zamani na intanet.

Shugaban UAE, Sheikh Mohamed bin Zayed Al Nahyan, tare da ministocin kasashen biyu, sun halarci sanya hannun kan yarjejeniyar da Tinubu ya bayyana a matsayin tarihi da dabarar bunkasa dangantakar kasashen biyu.

Tinubu ya bayyana cewa Investopia zai haɗa masu zuba jari, ‘yan kasuwa, masu kirkire-kirkire da masu tsara manufofi domin mayar da ra’ayoyi zuwa jarin da zai amfani al’umma, sannan ya ce Najeriya na da burin tara kusan dala biliyan 30 a duk shekara domin ayyukan sauyin yanayi da masana’antu masu kare muhalli, yana mai jaddada bukatar sauya tsarin hada-hadar kuɗin duniya domin sauƙaƙa wa ƙasashe masu tasowa samun jari ba tare da nauyin bashi ba.

Shugaban ƙasar ya kuma yi nuni da gyare-gyaren makamashi da tattalin arziki da gwamnatinsa ke aiwatarwa, ciki har da Dokar Lantarki ta 2023 da kuma manufofin kasuwar carbon, yana cewa hakan ya ƙara amincewar masu zuba jari.

Ya ƙara da cewa fitar da kayayyakin da ba na mai ba ya ƙaru da kashi 21 cikin 100, tare da alkawarin cewa Najeriya a shirye take ta yi aiki da abokan hulɗa domin gina ci gaba mai ɗorewa, adalci da amfani ga kowa.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Kungiyar Kiristoci Ta Wanke Gwamnan Bauchi Daga Zargin Ta’addanci
Next Post: Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo

Karin Labarai Masu Alaka

Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hankali Najeriya
Dakaru Sun Hallaka ’Yan Ta’adda Masu Yawa – DHQ Afrika
Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11 Najeriya
Shugaban Hukumar NAHCON Ya Ajeye Mukaminsa Labarai
Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
NUJ: Akwai Bukatar Inganta Albashin ‘Yan Jarida A Najeriya Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jiragen Saman Yakin Najeriya Suka Gurgunta Yunkurin Juyin Mulki A Benin Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Amurka Na Kokarin Watsi Da Tsohuwar Dokar Jones Labarai
  • Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya Amurka
  • Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO Labarai
  • Lauya Bala: Tabbas Kotu Zata Soke Zaben Shugaban PDP, Turaki Najeriya
  • ‘Yan Tawaye A Burkina Faso Sun Kashe ‘Yan Kasar Ghana Afrika
  • An Saka Dokar Hana Fita A Karamar Hukumar Lamurde Jihar Adamawa Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.