Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu Afrika
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa Afrika
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe Afrika
  • Masana Lafiya – Preeclampsia Cuta Ce Mai Hadari Amma Ana Iya Magance Ta Afrika

APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna
Published: May 23, 2026 at 10:52 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jam’iyyar APC a jihar Bauchi ta bayyana tsohon gwamnan jihar, Mohammed Abdullahi Abubakar, a matsayin ɗan takararta na gwamna a zaɓen shekarar 2027, bayan nasarar da ya samu a zaɓen fidda gwani da jam’iyyar ta gudanar.

An sanar da sakamakon zaɓen ne da sanyin safiyar Asabar daga bakin shugaban kwamitin gudanar da zaɓen fidda gwani na APC a Bauchi, tsohon mataimakin sufeton ‘yan sanda, John Bassey Abang, wanda ya ce an gudanar da zaɓen a ranar Juma’a 22 ga watan Mayun 2026 a faɗin jihar.

A cewarsa, M.A Abubakar SAN ya samu kuri’u dubu 57,517 inda ya doke sauran ‘yan takara shida da suka fafata a zaɓen. Tsohon Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Yusuf Maitama Tuggar, ya zo na biyu da kuri’u dubu 26,001, yayin da Nura Manu Soro ya samu kuri’u dubu 13,638.

Sauran waɗanda suka shiga takarar sun haɗa da Bala Maijama’a Wunti wanda ya samu kuri’u 13,648, Kabiru Baba Ma’aji mai kuri’u 8,157, Baba Abubakar Suleiman da ya samu kuri’u 7,688, sai Yakubu Yakubu Abdullahi da ya samu kuri’u 7,181.

Da yake bayyana sakamakon, shugaban kwamitin ya ce M.A Abubakar ya cika dukkan sharuɗɗan da ake buƙata, kuma ya samu mafi yawan ƙuri’un da aka kaɗa, saboda haka aka ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaɓen fidda gwani na APC a Bauchi.

Mohammed Abdullahi Abubakar ya taba zama gwamnan Jihar Bauchi tsakanin shekarun 2015 zuwa 2019 a ƙarƙashin jam’iyyar APC, kafin ya sha kaye a hannun gwamna mai ci yanzu, Bala Mohammed, na jam’iyyar PDP a zaɓen shekarar 2019.

Nasarar da tsohon gwamnan ya samu na nuni da cewa APC ta fara ɗaukar matakan tunkarar babban zaɓen 2027 a jihar Bauchi, yayin da ake sa ran za a fafata sosai tsakanin manyan jam’iyyun siyasa a jihar.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Masana Lafiya – Preeclampsia Cuta Ce Mai Hadari Amma Ana Iya Magance Ta
Next Post: Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Kasashen Duniya Sunyi Tir Da Hambarar Da Gwamnatin Venezuela Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
APC Ta Yi Babban Taron Amincewa Da Shugabannin Jam’iyyar Ba Hamayya Najeriya
Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Hadakar Ta Da Amurka Wajen Yakar ‘Yan Ta’adda Najeriya
NAHCON Ta Fitar Da Jadawalin Hajjin Bana 2027 Afrika
Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaban Amurka Yayi Barazanar Kulle Wani Dan Jarida Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano Najeriya
  • Sarkin Gombe Yayin Hawan Tudun Wada Labarai
  • An Bude Kamfanin Sarrafa Ma’adanai A Kasar Mozambique Labarai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Jamhuriyar Nijar Na Kokarin Inganta Harkokin Noman Kasar Afrika
  • ‘Yan Tawayen Houthi Sunkai Hari Isra’ila Afrika
  • Amurka Ta Bada Tabbacin Baiwa Ukraine Tsaron Na Shekaru 15 Amurka
  • Sabon Jadawalin Gasar Kwalon Kafa Ta Turai 2026 Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.