Jam’iyyar APC a jihar Bauchi ta bayyana tsohon gwamnan jihar, Mohammed Abdullahi Abubakar, a matsayin ɗan takararta na gwamna a zaɓen shekarar 2027, bayan nasarar da ya samu a zaɓen fidda gwani da jam’iyyar ta gudanar.
An sanar da sakamakon zaɓen ne da sanyin safiyar Asabar daga bakin shugaban kwamitin gudanar da zaɓen fidda gwani na APC a Bauchi, tsohon mataimakin sufeton ‘yan sanda, John Bassey Abang, wanda ya ce an gudanar da zaɓen a ranar Juma’a 22 ga watan Mayun 2026 a faɗin jihar.
A cewarsa, M.A Abubakar SAN ya samu kuri’u dubu 57,517 inda ya doke sauran ‘yan takara shida da suka fafata a zaɓen. Tsohon Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Yusuf Maitama Tuggar, ya zo na biyu da kuri’u dubu 26,001, yayin da Nura Manu Soro ya samu kuri’u dubu 13,638.
Sauran waɗanda suka shiga takarar sun haɗa da Bala Maijama’a Wunti wanda ya samu kuri’u 13,648, Kabiru Baba Ma’aji mai kuri’u 8,157, Baba Abubakar Suleiman da ya samu kuri’u 7,688, sai Yakubu Yakubu Abdullahi da ya samu kuri’u 7,181.
Da yake bayyana sakamakon, shugaban kwamitin ya ce M.A Abubakar ya cika dukkan sharuɗɗan da ake buƙata, kuma ya samu mafi yawan ƙuri’un da aka kaɗa, saboda haka aka ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaɓen fidda gwani na APC a Bauchi.
Mohammed Abdullahi Abubakar ya taba zama gwamnan Jihar Bauchi tsakanin shekarun 2015 zuwa 2019 a ƙarƙashin jam’iyyar APC, kafin ya sha kaye a hannun gwamna mai ci yanzu, Bala Mohammed, na jam’iyyar PDP a zaɓen shekarar 2019.
Nasarar da tsohon gwamnan ya samu na nuni da cewa APC ta fara ɗaukar matakan tunkarar babban zaɓen 2027 a jihar Bauchi, yayin da ake sa ran za a fafata sosai tsakanin manyan jam’iyyun siyasa a jihar.


