Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna
Published: May 23, 2026 at 10:52 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jam’iyyar APC a jihar Bauchi ta bayyana tsohon gwamnan jihar, Mohammed Abdullahi Abubakar, a matsayin ɗan takararta na gwamna a zaɓen shekarar 2027, bayan nasarar da ya samu a zaɓen fidda gwani da jam’iyyar ta gudanar.

An sanar da sakamakon zaɓen ne da sanyin safiyar Asabar daga bakin shugaban kwamitin gudanar da zaɓen fidda gwani na APC a Bauchi, tsohon mataimakin sufeton ‘yan sanda, John Bassey Abang, wanda ya ce an gudanar da zaɓen a ranar Juma’a 22 ga watan Mayun 2026 a faɗin jihar.

A cewarsa, M.A Abubakar SAN ya samu kuri’u dubu 57,517 inda ya doke sauran ‘yan takara shida da suka fafata a zaɓen. Tsohon Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Yusuf Maitama Tuggar, ya zo na biyu da kuri’u dubu 26,001, yayin da Nura Manu Soro ya samu kuri’u dubu 13,638.

Sauran waɗanda suka shiga takarar sun haɗa da Bala Maijama’a Wunti wanda ya samu kuri’u 13,648, Kabiru Baba Ma’aji mai kuri’u 8,157, Baba Abubakar Suleiman da ya samu kuri’u 7,688, sai Yakubu Yakubu Abdullahi da ya samu kuri’u 7,181.

Da yake bayyana sakamakon, shugaban kwamitin ya ce M.A Abubakar ya cika dukkan sharuɗɗan da ake buƙata, kuma ya samu mafi yawan ƙuri’un da aka kaɗa, saboda haka aka ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaɓen fidda gwani na APC a Bauchi.

Mohammed Abdullahi Abubakar ya taba zama gwamnan Jihar Bauchi tsakanin shekarun 2015 zuwa 2019 a ƙarƙashin jam’iyyar APC, kafin ya sha kaye a hannun gwamna mai ci yanzu, Bala Mohammed, na jam’iyyar PDP a zaɓen shekarar 2019.

Nasarar da tsohon gwamnan ya samu na nuni da cewa APC ta fara ɗaukar matakan tunkarar babban zaɓen 2027 a jihar Bauchi, yayin da ake sa ran za a fafata sosai tsakanin manyan jam’iyyun siyasa a jihar.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Masana Lafiya – Preeclampsia Cuta Ce Mai Hadari Amma Ana Iya Magance Ta
Next Post: Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Ambaliyar Ruwa Yayi Ajalin Mutane A Nairobi Afrika
Gombe Ta Yi Gasar Makarantun Firamare Don Bikin Cika Shekaru 100 Na Hassan Central Afrika
Shugaban Kasar Faransa Ya Zanta Da Shugaban Kasar Iran Afrika
An Kubutar Da Wani Wanda Mahaifinsa Ya daure Da Sarka Tsawon Shekaru 17 A Bauchi Labarai
An Bukaci Matasa Su Taka Gagarumar Rawa Wajen Gina Zaman Lafiya A Arewa Maso Gabas Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Fitaccen Dan Jarida a Sokoto Surajo Dalhatu Sifawa Ya Rasu Najeriya
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe Afrika
  • Iran Tana Duba Yiwuwar Cimma Yarjejeniya Da Amurka Afrika
  • Akwai Bukatar Nazari Game Da Dangantakar Iran Da Kasashen Gulf Amurka
  • Harin ‘Yan Daba Ya Hallaka Mutane 70 A Kasar Haiti Labarai
  • Sanata Goje: Sakamakon Zaben Daga Abuja Zai Fito Afrika
  • Al’ummomin da Ambaliyar Ruwan Mokwa a Jihar Nejan Najeriya ta sharewa gidaje sun Koka. Najeriya
  • NAHCON Ta Kaddamar da Tawagar Malamai Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.