Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika
  • Atiku Ya Bukaci Hadin Kan ‘Yan Adawa Domin Kawo Sauyi A Najeriya Afrika
  • Shugabannin Kiristoci Sun Halarci Filin Idi A Kaduna Domin Nuna Haɗin Kai Afrika
  • Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Bukaci Musulmi Su Rungumi Tausayi Da Ƙaunar Juna Afrika

Shugaban Kasar Faransa Ya Zanta Da Shugaban Kasar Iran
Published: April 12, 2026 at 8:48 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron yace ya zanta da shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian, ya kuma jaddada masa muhimmancin lafa rikici yayin tattaunawar tsagaita wuta a Pakistan.

Ba tabbacin ci gaba a tattaunawar sulhu

A cikin mabanbantan rahotanni da kafafen yada labarai daga jami’ain a Amurka da Iran, ya nuna cewa kasashen biyu basuyi kusa da cimma matasaya ba.

Kafin a fara tattaunawa, wani babban jami’i a Iran ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa Amurka ta yarda da zata saki kadarorin Iran da aka rike a Qatar da sauran bankunan dake wasu kasashe. Amma wani jami’in Amurka nan da nan ya musanta hakan.

Banda sakin kadarorin ta dake kasashen waje, fadar gwamnatin Tehran ta bukaci da ta mallaki ikon tafiyar da mashigin ruwa na Hormuz, da biyan diyyar yaki da kuma tsagaita wuta a yankin baki daya har da a kasar Lebanon a cewar jami’ai da kafar talabijin ta Iran.

A nasa bangaren bukatun da shugaban Amurka Donald Trump ya gabatar sun sha banban, mafi karancin su yace yana son a rika gudanar da wucewa da kayayyaki ta mashigin ruwan na Hormuz daga ko ina a duniya ba tare da fuskantar kalubale ba, da kuma dakile shirin makamashin nukiliya na Iran domin a tabbatar bazata iya hada atomic bomb ba.

Isra’ila, wadda ta hadu da Amurka wajen kaiwa Iran hari a yakin da aka fara shi ranar 28 ga Watan Fabrairu, ta kuma kasance tana sakarwa ‘yan kungiyar Hezbollah da Iran ke marawa baya bama-bamai a kasar Lebanon, ta kuma ce yakin da ake a Lebanon baya cikin yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Amurka da Iran.

Afrika, Amurka, Labarai, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Amurka Da Iran Sun Tattauna A Kasar Pakistan
Next Post: Kimanin Mutane 200 Ne Suka A Mutu A Wani Harin Jirgin Yakin Sojin Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Ankara Kai Wani Harin Bom Birnin Maiduguri Afrika
Kasashen Thailand Da Cambodia Sun Amince Da Tsagaita Wuta Labarai
Rundunar ‘Yan Sanda Sun Ceto Wani Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
China Ta Yi Kira Da Kasashen Gabas Ta Tsakiya Su Hada Kai Labarai
CAF Ta Hukunta Samuel Eto’o AFCON 2025 Labarai
Bangladesh Tasamu Rangwamen Harajin Da Amurka Ta Kakaba Mata Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi
  • Atiku Ya Bukaci Hadin Kan ‘Yan Adawa Domin Kawo Sauyi A Najeriya
  • Shugabannin Kiristoci Sun Halarci Filin Idi A Kaduna Domin Nuna Haɗin Kai
  • Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Bukaci Musulmi Su Rungumi Tausayi Da Ƙaunar Juna

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Farashin Danyen Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Afrika
  • Sakataren Tsaron Amurka Yace Baza’a Bayyana Bidiyon Kai Hari Akan Jirgin Ruwa Ba Amurka
  • Onana Ba Ya Cikin Tawagar Kamaru (AFCON) Wasanni
  • Tsohon Alkalin Alkalai A Najeriya Ya Rasu Yana Da Shekaru 71 Labarai
  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri Afrika
  • Jam’iyar APC A Jihar Gombe Ta Tsayar Da Jamilu Isiyaku Gwamna Takarar Gwamna Afrika
  • Akwai Bukatar APC Tayi Gyare-Gyare Kafun Zabe Afrika
  • Iran Tayi Allah Wadai Da Kai Hari Cibiyar Pars Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.