Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika

Shugaban Kasar Faransa Ya Zanta Da Shugaban Kasar Iran
Published: April 12, 2026 at 8:48 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron yace ya zanta da shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian, ya kuma jaddada masa muhimmancin lafa rikici yayin tattaunawar tsagaita wuta a Pakistan.

Ba tabbacin ci gaba a tattaunawar sulhu

A cikin mabanbantan rahotanni da kafafen yada labarai daga jami’ain a Amurka da Iran, ya nuna cewa kasashen biyu basuyi kusa da cimma matasaya ba.

Kafin a fara tattaunawa, wani babban jami’i a Iran ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa Amurka ta yarda da zata saki kadarorin Iran da aka rike a Qatar da sauran bankunan dake wasu kasashe. Amma wani jami’in Amurka nan da nan ya musanta hakan.

Banda sakin kadarorin ta dake kasashen waje, fadar gwamnatin Tehran ta bukaci da ta mallaki ikon tafiyar da mashigin ruwa na Hormuz, da biyan diyyar yaki da kuma tsagaita wuta a yankin baki daya har da a kasar Lebanon a cewar jami’ai da kafar talabijin ta Iran.

A nasa bangaren bukatun da shugaban Amurka Donald Trump ya gabatar sun sha banban, mafi karancin su yace yana son a rika gudanar da wucewa da kayayyaki ta mashigin ruwan na Hormuz daga ko ina a duniya ba tare da fuskantar kalubale ba, da kuma dakile shirin makamashin nukiliya na Iran domin a tabbatar bazata iya hada atomic bomb ba.

Isra’ila, wadda ta hadu da Amurka wajen kaiwa Iran hari a yakin da aka fara shi ranar 28 ga Watan Fabrairu, ta kuma kasance tana sakarwa ‘yan kungiyar Hezbollah da Iran ke marawa baya bama-bamai a kasar Lebanon, ta kuma ce yakin da ake a Lebanon baya cikin yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Amurka da Iran.

Afrika, Amurka, Labarai, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Amurka Da Iran Sun Tattauna A Kasar Pakistan
Next Post: Kimanin Mutane 200 Ne Suka A Mutu A Wani Harin Jirgin Yakin Sojin Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Kakakin Majalisar Kasar Amurka Yana Tsaka Mai Wuya Game Da Kasafin Kudi Amurka
Farashin Danyen Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Afrika
Amurka Da Tarayyar Turai Sun Fidda Sanarwa Afrika
Trump Yace Kawayen Amurka A Kungiyar NATO Basa Goyon Bayan Su Afrika
Kungiyar Kwadago Ta NLC Ta Gudanar Da Zanga-Zanga Bisa Matsalar Tsaro Tsaro
Zanga-Zangar Adawa Da Harin Amurka Da Isra’ila Ya Zamo Tarzoma A Pakistani Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Amurka Yayi Barazanar Kulle Wani Dan Jarida Amurka
  • Shugaban Hukumar Kwallon Kafa Ta Senegal Yaki Amincewa Da Hukuncin CFA Afrika
  • Shugaban Libya Ya Sayi Jirage Marasa Matuka Afrika
  • Shugabar Kungiyar Cinikayya Ta Duniya Ta Bukaci Kasashe Su Gyara Harkokin Cinikayya Afrika
  • Amurka Ta Kama Tsohon Ministan Kudin Kasar Ghana Afrika
  • Shugaban Hukumar Hana Yaduwar Cututtuka A Afirka Yace Akwai Rashin Fahimta A Tsakanin Kasashen Da Amurka Take Tallafawa Afrika
  • CAF Ta Ci Tarar Ƙasar Masar Dala 5,000 AFCON 2025 Wasanni
  • Majalisar Wakilai Ta Rikon Kwaryar Nijar Ta Gudanar Da Zama Karo Na Biyu Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.