Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Shugaban Kasar Faransa Ya Zanta Da Shugaban Kasar Iran
Published: April 12, 2026 at 8:48 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron yace ya zanta da shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian, ya kuma jaddada masa muhimmancin lafa rikici yayin tattaunawar tsagaita wuta a Pakistan.

Ba tabbacin ci gaba a tattaunawar sulhu

A cikin mabanbantan rahotanni da kafafen yada labarai daga jami’ain a Amurka da Iran, ya nuna cewa kasashen biyu basuyi kusa da cimma matasaya ba.

Kafin a fara tattaunawa, wani babban jami’i a Iran ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa Amurka ta yarda da zata saki kadarorin Iran da aka rike a Qatar da sauran bankunan dake wasu kasashe. Amma wani jami’in Amurka nan da nan ya musanta hakan.

Banda sakin kadarorin ta dake kasashen waje, fadar gwamnatin Tehran ta bukaci da ta mallaki ikon tafiyar da mashigin ruwa na Hormuz, da biyan diyyar yaki da kuma tsagaita wuta a yankin baki daya har da a kasar Lebanon a cewar jami’ai da kafar talabijin ta Iran.

A nasa bangaren bukatun da shugaban Amurka Donald Trump ya gabatar sun sha banban, mafi karancin su yace yana son a rika gudanar da wucewa da kayayyaki ta mashigin ruwan na Hormuz daga ko ina a duniya ba tare da fuskantar kalubale ba, da kuma dakile shirin makamashin nukiliya na Iran domin a tabbatar bazata iya hada atomic bomb ba.

Isra’ila, wadda ta hadu da Amurka wajen kaiwa Iran hari a yakin da aka fara shi ranar 28 ga Watan Fabrairu, ta kuma kasance tana sakarwa ‘yan kungiyar Hezbollah da Iran ke marawa baya bama-bamai a kasar Lebanon, ta kuma ce yakin da ake a Lebanon baya cikin yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Amurka da Iran.

Afrika, Amurka, Labarai, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Amurka Da Iran Sun Tattauna A Kasar Pakistan
Next Post: Kimanin Mutane 200 Ne Suka A Mutu A Wani Harin Jirgin Yakin Sojin Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Najeriya Zata Farfado Da Cibiyar Koyon Sana’oi Ta Dangote Afrika
Iran Zata Mayarwa Amurka Martanin Harin Kharg Afrika
Hari Da Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Mutane Da Dama A Darfur Labarai
Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka Ta Saka Takunkumi Visa Ga Wasu ‘Yan Rwanda Afrika
Sarkin Gombe Yayin Hawan Tudun Wada Labarai
Gwamnatin Tarayyar Najeriya Zata Raba Taki Ga Manoma Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Isra’ila Ta Cire Sunayen Wasu Mutane Biyu Cikin Wadanda Take Fako Afrika
  • An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe  Afrika
  • Pakistan Da Afghanistan Sun Shiga Kwana Na Biyar Suna Fafatawa Afrika
  • Al’ummomin da Ambaliyar Ruwan Mokwa a Jihar Nejan Najeriya ta sharewa gidaje sun Koka. Najeriya
  • Sabuwar Shekarar Musulunci 1448: Kiristoci Sun Yi Murna, Sunyi Kiran Samar Da Hutu Ga Shekarar Musulunci Afrika
  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe Afrika
  • Jami’an Tsaro Suna Farautar Wasu ‘Yan Ta’adda A Najeriya Afrika
  • Amurka Zatayi Amfani Da Sansanonin Birtaniya Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.