Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Najeriya Zata Farfado Da Cibiyar Koyon Sana’oi Ta Dangote
Published: April 1, 2026 at 3:46 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: April 1, 2026

Gwamnatin tarayyar Najeriya da ta jihar Kano da kuma gidauniyar rukunin kamfanonin Dangote, sun cimma yarjejeniyar haɓakawa, tare da kula da babbar cibiyar koyon sana’o’i ta Dangote (Dangote Ultramodern Skills Acquisition Center) da ke birnin Kano.

Wannan mataki dai na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Hukumar Ilimin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano (STSB), Farfesa Dahiru Sale Mohammed, ya fitar a madadin Kwamishinan Ilimi na jihar.

A karkashin wannan sabuwar dangantaka, ɓangarorin uku za su dauki nauyin garambawul da inganta kayan aikin cibiyar, sannan su tabbatar da dorewar ayyukanta na tsawon shekaru 20 masu zuwa.

Cibiyar, wacce aka gina domin bai wa matasa horo kan kwarewar hannu da fasahar zamani, ana sa ran za ta kasance kashin baya wajen rage radadin rashin aikin yi a jihar ta Kano da ma makwabtanta.

Farfesa Dahiru Sale ya bayyana cewa wannan yunkuri zai tabbatar da cewa cibiyar ba ta durkushe ba kamar yadda wasu ayyukan ke yi idan aka samu canjin gwamnati, duba da tsarin kula da ita na dogon lokaci da aka kulla.

Jihar Kano dai ita ce jiha mafi yawan jama’a a arewacin Najeriya, inda matasa ke da kaso mafi tsoka. Wannan cibiya za ta mayar da hankali ne wajen koyar da sana’o’in da suka dace da bukatun karni na 21, domin ba wa matasa damar dogaro da kansu maimakon jiran aikin gwamnati.

Sanarwar ta jaddada cewa an kammala dukkan shirye-shiryen fara aikin fito da sabuwar fuskar cibiyar nan ba da jimawa ba.

Afrika, Labarai, Najeriya, Sana'o'i

Post navigation

Previous Post: Rashin Kyawun Hanyoyi Babbar Matsalace A Najeriya
Next Post: Mabiya Dariqar Tijjaniyya Sunfara Gudanar Da Addu’oi Saboda Tsare Sheikh Sani Khalifa Zariya

Karin Labarai Masu Alaka

Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hankali Najeriya
Wasan Hamayya (Istanbul Derby) Fenerbahçe Da Galatasaray 1-1 Labarai
Mayakan RSF Sun Zafafa Kai Hare Hare Da Jirgi Maras Matuki A Sudan Labarai
An Garkame Wani Babban Soja A Kasar Australiya Afrika
Kungiyar Mata Manoma A Najeriya Ta Raba Kyautar Abinci A Gombe Afrika
Harin ‘Yan Daba Ya Hallaka Mutane 70 A Kasar Haiti Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz
  • Shugaba Tinubu Yasa Hannu Kan Dokar Kasafin 2026
  • Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba
  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Jihar Gombe Ta Haramta Sana’ar Bola Jari Tsaro
  • Hawan Sallah A Jihar Katsina Afrika
  • Gwamna Ahmad Aliyu Na Jihar Sokoto Ya Gabatar Da Kasafin Fiye Da Naira Biliyan 700 Labarai
  • Tattalin Arzikin Kasar Congo Ya Bunkasa Labarai
  • Kudi Sunfi Rayuwar Mutum Muhimmanci A Asibitocin Najeriya Kiwon Lafiya
  • Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya Afrika
  • Gwamnatin Jamhuriyar Nijar Na Kokarin Inganta Harkokin Noman Kasar Afrika
  • Amurka Ta Cire Takunkumin Da Ta Kakabawa Shugaban Venezuela Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.