Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata Afrika
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa Afrika
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno Amurka
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe Afrika
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya Afrika

Gwamnatin Najeriya Zata Farfado Da Cibiyar Koyon Sana’oi Ta Dangote
Published: April 1, 2026 at 3:46 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: April 1, 2026

Gwamnatin tarayyar Najeriya da ta jihar Kano da kuma gidauniyar rukunin kamfanonin Dangote, sun cimma yarjejeniyar haɓakawa, tare da kula da babbar cibiyar koyon sana’o’i ta Dangote (Dangote Ultramodern Skills Acquisition Center) da ke birnin Kano.

Wannan mataki dai na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Hukumar Ilimin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano (STSB), Farfesa Dahiru Sale Mohammed, ya fitar a madadin Kwamishinan Ilimi na jihar.

A karkashin wannan sabuwar dangantaka, ɓangarorin uku za su dauki nauyin garambawul da inganta kayan aikin cibiyar, sannan su tabbatar da dorewar ayyukanta na tsawon shekaru 20 masu zuwa.

Cibiyar, wacce aka gina domin bai wa matasa horo kan kwarewar hannu da fasahar zamani, ana sa ran za ta kasance kashin baya wajen rage radadin rashin aikin yi a jihar ta Kano da ma makwabtanta.

Farfesa Dahiru Sale ya bayyana cewa wannan yunkuri zai tabbatar da cewa cibiyar ba ta durkushe ba kamar yadda wasu ayyukan ke yi idan aka samu canjin gwamnati, duba da tsarin kula da ita na dogon lokaci da aka kulla.

Jihar Kano dai ita ce jiha mafi yawan jama’a a arewacin Najeriya, inda matasa ke da kaso mafi tsoka. Wannan cibiya za ta mayar da hankali ne wajen koyar da sana’o’in da suka dace da bukatun karni na 21, domin ba wa matasa damar dogaro da kansu maimakon jiran aikin gwamnati.

Sanarwar ta jaddada cewa an kammala dukkan shirye-shiryen fara aikin fito da sabuwar fuskar cibiyar nan ba da jimawa ba.

Afrika, Labarai, Najeriya, Sana'o'i

Post navigation

Previous Post: Rashin Kyawun Hanyoyi Babbar Matsalace A Najeriya
Next Post: Mabiya Dariqar Tijjaniyya Sunfara Gudanar Da Addu’oi Saboda Tsare Sheikh Sani Khalifa Zariya

Karin Labarai Masu Alaka

Al’ummar Jihar Nasarawa Suna Cecekuce Bisa Tsaida Aliyu Wadada Takarar Gwamna Afrika
Akwai Alamar Shawarwari Tsakanin Amurka Da Turai Zai Kawo Karshen Yakin Rasha Amurka
Mun Kwato Kimanin Naira Biliyan 40 Na Badakala A Tsawon Shekara Daya Labarai
Netanyahu Yana Neman Shawarwari Daga Hukumomin Lebanon Labarai
Shugaban Kasar Faransa Ya Zanta Da Shugaban Kasar Iran Afrika
Dangote Ya Bukaci ICPC Ta Binciki Shugaban NMDPRA Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ƙungiyoyin Ƙwadago Sun Ce Albashin ₦70,000 Ya Gaza Biyan Bukatun Ma’aikata
  • NUJ Gombe Ta Ƙarfafa Bin Ɗa’a A Aikin Jarida, Ta Kaddamar Da Kwamitin Ladabtarwa
  • Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno
  • Masu Ruwa Da Tsaki Sun Buƙaci Ƙarin Tallafi Ga Iyaye Mata Masu Shayarwa A Gombe
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Yi Gargaɗi Ga Masu Karya Dokokin Hanya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasashe Biyar Zasu Tura Sojoji Domin Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya A Gaza Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hukumar MDD Tace Wadanda Suka Mutu A Harin Sudan Sun Haura 70 Afrika
  • Masar Ta Kayyade Farashin Buradi A Kasar Afrika
  • Jirgin Ruwa Ya Kife A Yammacin Kasar Gambiya Labarai
  • Zaman Lafiya Yafara Dawowa A Sudan Afrika
  • Gwamnatin Shugaba Trump Tana Cigaba Da Janye Jakadunta Zuwa Gida Amurka
  • ‘Yansandan Uganda Sun Tsare ‘Yar Fafutukar Kare Hakkin Bil’adama Sarah Bireete Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar China Tana Cigaba Da Nuna Fin Karfi Ga Kasar Taiwan Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.