Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gombe Ta Ƙarfafa Matasa da Ƙwarewar da Za Ta Kai Su Masana’antar Mai Da Iskar Gas Afrika
  • Jihar Gombe Ta Karbi Bakuncin Taron Tsaro Tsakanin DIG Da Masu Ruwa Da Tsaki Afrika
  • Sauya Sunan Lafarge Africa Zuwa HBM Nigeria Plc Zai Samar Da Cigaba – Sarkin Fulanin Gombe Afrika
  • An Karrama Darakta Janar Na DSS Bisa Ƙoƙarinsa Na Inganta Alaƙar Hukumomin Tsaro Da Kafafen Yaɗa Labarai Afrika
  • Gwamnatin Tarayyar Najeriya Zata Raba Taki Ga Manoma Afrika

NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa
Published: June 23, 2026 at 9:06 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: June 23, 2026

Hukumar Alhazai ta Najeriya wato (NAHCON) ta sanar da kammala jigilar alhazan Najeriya daga Kasar Saudiyya bayan gudanar da aikin Hajjin bana na 2026, inda ake sa ran jirgi na karshe da ke dauke da alhazan Jihar Zamfara zai sauka a Najeriya a yau, 23 ga Yuni, 2026.

Da wannan ne aka rufe shafin ayyukan Hajjin 2026 gaba daya, bayan nasarar jigilar dubban alhazan Najeriya zuwa kasa mai tsarki da kuma dawo da su gida lafiya.

Sai dai hukumar ta bayyana cewa akwai alhazai ’yan Najeriya 12 da ke ci gaba da karbar magani a wasu asibitoci daban-daban da ke Saudiyya sakamakon matsalolin lafiya.

NAHCON ta ce tana sa ido sosai kan halin da suke ciki tare da shirya yadda za a dawo da su Najeriya cikin aminci da zarar an sallame su daga asibiti.

Shugaban NAHCON, Ambasada Ismail Abba Yusuf, ya mika godiya ga Allah Madaukakin Sarki bisa nasarar da aka samu a aikin Hajjin bana. Haka kuma ya yaba wa Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, da Mataimakinsa, Sanata Kashim Shettima, bisa goyon baya da hadin kan da suka bayar wanda ya taimaka wajen samun nasarar aikin.

Hukumar ta kuma gode wa Hukumomin Jin Dadin Alhazai na Jihohi, kamfanonin yawon Hajji masu lasisi, masu samar da ayyuka, kamfanonin jiragen sama, ma’aikatan lafiya, jami’an tsaro, kafafen yada labarai da kuma alhazan Najeriya saboda gudunmawar da suka bayar wajen gudanar da aikin.

NAHCON ta amince cewa kamar yadda ake samu a manyan ayyuka irin wannan, an fuskanci wasu kalubale a yayin gudanar da Hajjin. Sai dai ta ce an dauki darussa masu muhimmanci daga abubuwan da suka faru, kuma za a yi amfani da su wajen inganta ayyukan Hajji a nan gaba.

A wani bangare kuma, hukumar ta sanar da fara shirye-shiryen Hajjin shekarar 1448H/2027 tun kafin kammala dukkan ayyukan bana. A cewar hukumar, an sanar da dukkan masu ruwa da tsaki a harkar Hajji ta wata takarda mai dauke da kwanan watan 15 ga Yuni, 2026, mai taken “Fara Shirye-shiryen Hajjin 1448H/2027” wadda Sakataren Hukumar, Dakta Mustapha Muhammad Ali, ya sanya wa hannu a madadin Shugaban NAHCON.

Saboda haka, hukumar ta umarci Hukumomin Jin Dadin Alhazai na Jihohi da kamfanonin yawon Hajji masu zaman kansu da su fara shirye-shiryensu nan take bisa tsarin da Ma’aikatar Hajji da Umrah ta Saudiyya ta gindaya domin Hajjin shekarar 2027.

NAHCON ta ce daukar matakan tun da wuri zai taimaka wajen kara inganta shirye-shiryen Hajji da kuma tabbatar da samun nasara mafi girma a shekarun da ke tafe.

Amurka, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Dan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar APM A Bauchi Ya Bada Gudummawar Naira Miliyan ₦21 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Bara Da Shira

Karin Labarai Masu Alaka

Hamas Ta Kwance Damara Afrika
Shugaban Ukraine Ya Tattauna Da Trump Akan Zaman Lafiya Amurka
Gwamnatin Gombe Ta Kulla Yarjejeniyar Da New Zealand Kimiya
Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai
Gwamnatin Bauchi Ta Amince Domin Inganta Kasuwancin Nama A Jihar Labarai
Mahaifiyar Nasiru El Rufai Ta Rasu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa
  • Dan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar APM A Bauchi Ya Bada Gudummawar Naira Miliyan ₦21 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Bara Da Shira
  • Idan Allah Yasa Muka Kafa Gwamnati Zamu Kyautata Wa Ma’aikata Yakubu Adamu Dan Takarar Kujeran Gwamnan Bauchi
  • Gombe Ta Ƙarfafa Matasa da Ƙwarewar da Za Ta Kai Su Masana’antar Mai Da Iskar Gas
  • Jihar Gombe Ta Karbi Bakuncin Taron Tsaro Tsakanin DIG Da Masu Ruwa Da Tsaki

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tsarin Haraji Mai Cike Da Ayoyin Tambaya Na Shirin Fara Aiki Labarai
  • Wata Biyu Najeriya Bata Bada Lasisin Shigo Da Mai Daga Ketare Ba Labarai
  • Hukumar Tsaron Civil Defence A Gombe Ta Samar Da Jami’ai Don Tabbatar Da Tsaro A Bukukuwan Karshen Shekara Labarai
  • Farashin Mai Ya Doshi Dala 100 Kowacce Ganga Afrika
  • Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa Najeriya
  • Fiye Da Mutane Miliyan Hudu Suna Fuskantar Barazanar Yunwa A Somaliya Sauran Duniya
  • Sanata Barau Ya Raba Motoci Da Babura Ga Al’ummar Kano Ta Arewa Afrika
  • Tinubu Ya Sayi Fom Din Takarar Shugaban Kasa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.