Hukumar Alhazai ta Najeriya wato (NAHCON) ta sanar da kammala jigilar alhazan Najeriya daga Kasar Saudiyya bayan gudanar da aikin Hajjin bana na 2026, inda ake sa ran jirgi na karshe da ke dauke da alhazan Jihar Zamfara zai sauka a Najeriya a yau, 23 ga Yuni, 2026.
Da wannan ne aka rufe shafin ayyukan Hajjin 2026 gaba daya, bayan nasarar jigilar dubban alhazan Najeriya zuwa kasa mai tsarki da kuma dawo da su gida lafiya.
Sai dai hukumar ta bayyana cewa akwai alhazai ’yan Najeriya 12 da ke ci gaba da karbar magani a wasu asibitoci daban-daban da ke Saudiyya sakamakon matsalolin lafiya.
NAHCON ta ce tana sa ido sosai kan halin da suke ciki tare da shirya yadda za a dawo da su Najeriya cikin aminci da zarar an sallame su daga asibiti.
Shugaban NAHCON, Ambasada Ismail Abba Yusuf, ya mika godiya ga Allah Madaukakin Sarki bisa nasarar da aka samu a aikin Hajjin bana. Haka kuma ya yaba wa Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, da Mataimakinsa, Sanata Kashim Shettima, bisa goyon baya da hadin kan da suka bayar wanda ya taimaka wajen samun nasarar aikin.
Hukumar ta kuma gode wa Hukumomin Jin Dadin Alhazai na Jihohi, kamfanonin yawon Hajji masu lasisi, masu samar da ayyuka, kamfanonin jiragen sama, ma’aikatan lafiya, jami’an tsaro, kafafen yada labarai da kuma alhazan Najeriya saboda gudunmawar da suka bayar wajen gudanar da aikin.
NAHCON ta amince cewa kamar yadda ake samu a manyan ayyuka irin wannan, an fuskanci wasu kalubale a yayin gudanar da Hajjin. Sai dai ta ce an dauki darussa masu muhimmanci daga abubuwan da suka faru, kuma za a yi amfani da su wajen inganta ayyukan Hajji a nan gaba.
A wani bangare kuma, hukumar ta sanar da fara shirye-shiryen Hajjin shekarar 1448H/2027 tun kafin kammala dukkan ayyukan bana. A cewar hukumar, an sanar da dukkan masu ruwa da tsaki a harkar Hajji ta wata takarda mai dauke da kwanan watan 15 ga Yuni, 2026, mai taken “Fara Shirye-shiryen Hajjin 1448H/2027” wadda Sakataren Hukumar, Dakta Mustapha Muhammad Ali, ya sanya wa hannu a madadin Shugaban NAHCON.
Saboda haka, hukumar ta umarci Hukumomin Jin Dadin Alhazai na Jihohi da kamfanonin yawon Hajji masu zaman kansu da su fara shirye-shiryensu nan take bisa tsarin da Ma’aikatar Hajji da Umrah ta Saudiyya ta gindaya domin Hajjin shekarar 2027.
NAHCON ta ce daukar matakan tun da wuri zai taimaka wajen kara inganta shirye-shiryen Hajji da kuma tabbatar da samun nasara mafi girma a shekarun da ke tafe.


