Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika

Tinubu Ya Sayi Fom Din Takarar Shugaban Kasa
Published: April 28, 2026 at 2:28 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazaɓar Ikeja a jihar Legas, James Faleke, ya karɓi fom ɗin na gani Ina so da na tsayawa takara na jam’iyyar APC a madadin Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu gabanin zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027.

Majiyoyi sun rawaito cewa, sakataren tsare-tsare na ƙasa na APC, Suleiman Argungu, ne ya bayyana fara wannan tsari na siyar da fom a ranar Talata a Abuja, inda ya miƙa fom ɗin ga Faleke, wanda kuma shi ne wanda ya kafa ƙungiyoyin goyon bayan Tinubu.

Rahotanni sun nuna cewa Faleke ya biya kuɗin fom ɗin da ya kai naira miliyan 100 a madadin shugaban ƙasar, abin da ke nuna fara shirye-shiryen neman sake zaɓen Tinubu a hukumance.

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa, INEC, ta tsara gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na majalisar tarayya a ranar Asabar, 16 ga Janairu, 2027, yayin da zaɓen gwamna da na majalisun jihohi za su gudana a ranar 6 ga Fabrairu, 2027.

Haka kuma, hukumar ta sanar da cewa za a gudanar da zaɓen fidda gwani na jam’iyyun siyasa daga ranar 23 ga Afrilu, 2026 zuwa 30 ga Mayu, 2026, tare da warware duk wata takaddama da ka iya tasowa a wannan lokaci.

INEC ta kuma bayyana cewa yaƙin neman zaɓe na shugabancin ƙasa da na majalisar tarayya zai fara ne daga ranar 19 ga Agusta, 2026, yayin da na gwamna da na majalisun jihohi zai fara daga ranar 9 ga Satumba, 2026.

Ana sa ran ƙarin bayani zai biyo baya kan wannan lamari.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Najeriya Ta Jinjinawa Saudiya
Next Post: NAHCON Ta Fitar Da Jadawalin Hajjin Bana 2027

Karin Labarai Masu Alaka

Kungiyar Cigaban Al’ummar Tangale Tace Bata Goyon Bayan Kai Ziyara Wa Gwamnan Gombe Labarai
Tinubu Ya Bayyana ‘Yan Bindiga Da Cewa Ruwa Yakarewa Dan Kada Afrika
An Samu Nasarar Karbo Karin Yara 130 Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Yiwa Dokokin Kare Hakkin Yara Rikon Sakainar Kashi Labarai
Kungiyoyin Mata A Jihar Filato Sunyi Gangamin Samun Jagorancin Siyasa Afrika
Tarayyar Turai Zasu Kirkiro Sojojin Haɗin Gwiwa Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dakarun Tsaron Ruwan Amurka Sunfara Killace Hanyoyi Amurka
  • Shugaba Trump Ya Janye Karbar Kudin Fito Daga Wasu Kasashen Turai Amurka
  • Gwamnatin Afirka Ta Kudu Na Kokarin Kafa Wasu Dokoki A Kasar Labarai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Samu Nasarar Ceto Wasu Daliban St. Mary’s Tsaro
  • Baitul Malin Amurka Zata Bawa Venezuela Da Cuba Damar Sayar Da Mai Amurka
  • Donald Trump Yace Basu Cimma Matsaya Da Benjamin Natanyahu Ba Afrika
  • Rahoton Leken Asiri Yanuna Cewa Harin Amurka Bazai Samar Da Shugabanci A Iran Ba Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.