Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Wani Abu Ya Fashe A Asibitin Bagudo Dake Jihar Kebbi
Published: December 30, 2025 at 8:42 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 30, 2025

Rundunar ‘yan sanda a jihar Kebbi ta tabbatar da afkuwar fashewar bam da sanyin safiyar Talata a babban asibitin Bagudo, da ke karamar hukumar Bagudo ta jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, SP Bashir Usman, ya fitar a Birnin Kebbi.

Usman ya ce: “Muna son tabbatarwa mazauna yankin cewa an shawo kan al’amuran tsaro gaba ɗaya bayan wata babbar kara ta fashewa da ta auku a babban asibitin Bagudo da sanyin safiyar Talata, 30 ga Disamba.

“Ƙungiyar tsaro ta haɗin gwiwa wadda ta ƙunshi ‘yan sanda, sojoji da ‘yan sa kai ta kulle tare da tabbatar da tsaron yankin cikin gaggawa. Ƙwararrun jami’an EOD-CBRN suna wurin suna gudanar da cikakken bincike.

“Muna farin cikin sanar da cewa babu wanda ya rasa ransa. Duk da cewa wani gini a bangaren ma’aikata ya lalace, mazauna wajen sun riga sun fice lafiya.

“Kwamishinan ‘yan sanda na jihar ya ƙara tura jami’an tsaro na musamman domin tabbatar da zaman lafiya da doka.”

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Kasar China Ta Kaddamar Da Rawar Daji A Yankin Taiwan
Next Post: An Gudanar Da Jana’izar ’Yan Jaridan Da Suka Rasu A Jihar Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Kungiyar ‘Yan Ta’adda Masu Alaka Da ISIS Sun Kashe Mutane A Congo Tsaro
Ukraine Takai Hari Wajen Kera Makami Mai Linzami A Rasha Labarai
Rundunar Tsaro Suna Cigaba Da Nasara Akan ‘Yan Ta’adda Tsaro
Jami’in Diflomasiyyar Da Ake Zargi Da Kisan Prime minister Ya Daukaka Kara Afrika
‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji A Jihar Kebbi Afrika
Iran Tana Duba Yiwuwar Cimma Yarjejeniya Da Amurka Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Alaka Na Cigaba Da Kamari Tsakanin Rwanda Da Barundi Labarai
  • Hukumar EFCC Ta Kwace Gidan Tsohon Antoni Janar Abubakar Malami Najeriya
  • Babu Dabbar Da Zata Sake Shiga Amurka Daga Mexico! Amurka
  • Gwamnatin Jihar Neja Ta Soke Lasisin Mallakar Wasu Manyan Filaye A Jihar Labarai
  • Gwamnatin Sham Tace Harin Kurdawa Ya Hallaka Sojojin Kasar Afrika
  • Isra’ila Takai Hare Hare Birnin Tehran Afrika
  • Hukumar ICPC Ta Gayyaci Dangote Labarai
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Kauyuka Dake Yammacin A Najeriya Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.