Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Hamma Saleh Ya Yi Fatali da Bai Wa Pantami Takarar Gwamna a PDP Afrika
  • Ferfesa Pantami Yasamu Tikitin Takarar Gwamnan Gombe A Jami’yar PDP Afrika
  • Kotu A Abuja Tabawa Goodluck Jonathan Daman Tsayawa Takara Afrika
  • Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya Afrika
  • Muhimmin Sako Ga Alhazai Dake Kasar Saudiya Afrika

Iran Tace Dole A Tsagaita Wuta A Lebanon Kafun Fara Shawarwari
Published: April 11, 2026 at 11:22 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

A ranar  juma’a Iran tace tilas a sakamarta kadarorinta, kuma a tsagaita wuta a Lebanon, kamun ta fara shawarwari da Washington, mataki da ya jefa zaman sulhu da za’a fara yau Asabar, cikin rashin tabbas.

Kakakin majalisar dokokin kasar Mohammed Baqeer Qaibaf ya fada a shafinsa a dandalin X cewa, wadannan bukatu biyu dama an amince da su a magana da suka yi da Washington, saboda haka ba za’a fara shawarwari ba har sai an cikata alkawuran, yayinda ake ci gaba da takaddama kan ainihin sharuddan tsagaita wuta.

Shi ma ministan harkokin wajen kasar Abbas Araqchi, ya jaddada haka, ya bukaci da a kawo karshen farmakin da Isra’ila take kaiwa a Lebanon. Ana sa ran duka jami’an biyu na Iran za su kasance a wajen zaman shawarwari da za’a yi, kamar yadda wasu majiyoyi biyu a Pakistan suka fada.

Kodashike babu wani martani nan take daga fadar White house, shugaban Amurka Donald Trump ya fada a wani sako da ya wallafa a shafinsa dandalin sada zumunta da ake kira Truth Social, dalili daya da ya sa har yanzu Farisawan suke da rai shine domin a kulla yarjejeniya da su.

Shugaba Trump wanda bai maida martani kai tsaye kan bukatun da Iran ta gabatar ba, ya gayawa wata jaridar Amurka da ake kira New York Post, cewa, jiragen ruwan yaki ana sake musu shiri da albarusai masu kwari domin su ci gaba da kai farmaki kan Iran, muddin shawarwarin sulhu da za’a yi Iran a Pakistan ya ci tura.

Mataimaki shugaban Amurka JD Vance wanda zai jagoranci tawagar Amurka zuwa taron, yace yana fatan za’a sami kyakyawar sakamakon taron da za su yi, ya kara da cewa, “Idan kuma za su kokarin su yaudare mu, za su fuskanci turjiya daga tawagar.”

Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Hari Da Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Mutane Da Dama A Darfur
Next Post: Mataimakin Shugaban Amurka Ya Sauka A Islamabad Domin Tattaunawa

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnan Jihar Gombe Ya Umurci A Rufe Makarantu Labarai
Najeriya Da Amurka Sun Karfafa Alakar Tsaro Afrika
Shugabar Hamayya A Venezuela Ta Gana Da Paparoma Leo Amurka
Kawayen Amurka Bazasu Shiga Matakin Shugaba Trump Ba Amurka
Gwamnatin Sham Tace Harin Kurdawa Ya Hallaka Sojojin Kasar Afrika
An Maka Wasu Jami’an Immigration A Kotu Bisa Zargin Rashin Da’a A Birtaniya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hamma Saleh Ya Yi Fatali da Bai Wa Pantami Takarar Gwamna a PDP
  • Ferfesa Pantami Yasamu Tikitin Takarar Gwamnan Gombe A Jami’yar PDP
  • Kotu A Abuja Tabawa Goodluck Jonathan Daman Tsayawa Takara
  • Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya
  • Muhimmin Sako Ga Alhazai Dake Kasar Saudiya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Na Shirin Kauracewa Taron Kungiyar Kasashen G20 Afrika
  • Kamfanin Dangote Zai Sayo Na’urori Daga Kasar China Kimiya
  • Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique Afrika
  • Kasar Tanzaniya Zata Gina Babban Tashar Iskar Gas Labarai
  • Kamfanin Bitcoin A Korea Ta Kudu Yayi Kuskuren Turawa Masu Mu’amala Da Kamfanin Kudade Afrika
  • Amurka Na Gargadin Rwanda Da Ta Mutunta Alkawali Afrika
  • Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Kashe-kashen Jos Da Kaduna Afrika
  • Shugaban Libya Ya Sayi Jirage Marasa Matuka Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.