Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Hukumar NDLEA Ta Lalata Gonakin Wiwi A Ekiti
Published: June 26, 2026 at 9:28 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA) ta bayyana cewa ta lalata gonakin wiwi masu fadin sama da hekta 51 tare da kama mutane 281 da ake zargi da safarar miyagun kwayoyi, sayarwa da kuma amfani da su a jihar Ekiti cikin shekara guda.

Kwamandan NDLEA na jihar, Rufus Aina, ne ya bayyana hakan a Ado Ekiti yayin bikin Ranar Yaki da Miyagun Kwayoyi ta Duniya ta 2026.

Ya ce hukumar ta samu nasarar gurfanar da mutane 50 da aka yanke musu hukunci, yayin da sauran shari’o’i ke gaban Kotun Tarayya da ke Ado Ekiti.

Aina ya ce noman wiwi a sassa daban-daban na jihar na ci gaba da zama babban kalubale, yana mai gargadin cewa safara da amfani da miyagun kwayoyi na haddasa aikata laifuka, rashin tsaro, barin makaranta da kuma lalata rayuwar al’umma.

Ya kara da cewa cikin shekara guda da ta gabata, hukumar ta gudanar da gangamin wayar da kai 76 da shirye-shiryen rediyo da talabijin 15, tare da ba mutane 87 masu amfani da miyagun kwayoyi shawara da jinya.

Har ila yau, ya bayyana cewa an kwato miyagun kwayoyi masu nauyin kilogram 6,337.517, yayin da wani mutum mai suna Osho Akindele ya samu daurin shekaru 20 a gidan yari saboda laifukan da suka shafi miyagun kwayoyi.

Kwamandan ya kuma bayyana cewa an kama wasu tsofaffi biyu masu shekaru 78 da 80 bisa zargin mallaka da safarar miyagun kwayoyi, yana kira ga al’umma da su hada kai da hukumomi wajen yaki da matsalar miyagun kwayoyi.

Afrika, Kiwon Lafiya, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Shugaban Miyetti Allah Zai Fuskanci Shari’a Kan Zargin Badakalar Kuɗi da Ta’addanci
Next Post: Gwamnatin Gombe Ta Kaddamar Da Sabon Ofishin GOGIS Don Inganta Tsarin Filaye

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Trump Yace Tehran Tana Neman Kulla Alaka Da Washington Amurka
‘Yan Tada Kayar Baya Sun Tayar Da Bom A Maiduguri Labarai
Na Yi Murabus Ne Don Amurka Ta Keta Haddin Iraniyawa Amurka
Jaura Ta Bayyana A Wasu Jihohin Amurka Labarai
Majalisar Wakilai Tayi Allah Wadai Da Hare-Haren ‘Yan Bindiga A Gombe Labarai
Netanyahu Yana Neman Shawarwari Daga Hukumomin Lebanon Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Tace Ta Farmaki Mayakan ISIS A Jihar Sokoto Labarai
  • Rundunar ‘Yan Sanda Sun Ceto Wani Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
  • ‘Yan Sandan Habasha Sun Kama Dubban Albarusai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Zata Fice Daga Iran Cikin Gaggawa Afrika
  • Najeriya Zata Kara Mai Da Take Hakowa Afrika
  • Masar Ta Jibge Jiragen Yaki Marasa Matuka Afrika
  • Zulum Ya Tallafa Wa Mambobin NYSC Da Naira Miliyan 8.2 A Borno Afrika
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.