Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika

Gwamnatin Tarayya Tayi Baje Kolin Nasarorin Tinubu
Published: April 24, 2026 at 3:51 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bayyana cewa Najeriya ta shiga wani sabon babi na gyara da ci gaba a ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, inda ta buƙaci kafofin yaɗa labarai na duniya da su riƙa rahoton gaskiyar abin da ke faruwa a ƙasar.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Alhaji Mohammed Idris, ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis yayin wata tattaunawa ta musamman da wakilan gidajen jaridun ƙasashen waje a Abuja.

Ministan ya bayyana cewa a shekarar 2025, tattalin arzikin Nijeriya ya haɓaka da kashi 3.87 cikin ɗari, wanda hakan ke nuna cewa ci gaban tattalin arzikin ya fi ƙaruwar yawan jama’a sauri a karon farko cikin kusan shekara goma.

A cewarsa, cire tallafin man fetur da gyara tsarin musayar kuɗi sun taimaka kwarai wajen tara kuɗaɗen da ake amfani da su yanzu wajen samar da manyan ayyuka da inganta rayuwar al’umma.

Alhaji Mohammed Idris ya jero wasu daga cikin muhimman nasarorin da aka samu, waɗanda suka haɗa da:
• Samar da lamunin karatu ga ɗalibai ta hanyar asusun NELFUND.
• Inganta harkar tsaro ta hanyar amfani da bayanan sirri da leken asiri.
• Yunkurin kafa ’yan sandan jihohi domin bai wa hukumomin gida yancin cin gashin kansu.
• Zuba jari a fannin noma da fasahar zamani domin samar wa matasa ayyukan yi.

A nasa jawabin, Ministan Kuɗi da Tattalin Arziki, Mista Taiwo Oyedele, ya bayyana cewa Nijeriya ta fita daga yanayin fargaba, yanzu tana matakin tabbatar da cewa al’umma sun fara jin daɗin waɗannan gyare-gyare a cikin rayuwarsu ta yau da kullum.

Haka ita ma Ministar Masana’antu da Kasuwanci, Dr. Jumoke Oduwole, ta jaddada cewa Nijeriya ba kawai tana binsu a bayan Afirka ba ne, tana kokarin zama jagora ne a fannin ciniki da masana’antu a faɗin nahiyar.

Minista Idris ya rufe jawabin nasa da kira ga ’yan jaridun duniya da su riƙa bayyana gaskiya game da Nijeriya.

Ya ce: “Muna son a riƙa bayyana nasarorinmu da kuma ƙalubalen da muke fuskanta duka tare, domin hakan ne kawai zai nuna ainihin hoton Nijeriya.”

Taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati da suka haɗa da Bayo Onanuga da Sunday Dare da kuma Abdulaziz Abdulaziz, waɗanda duka ke tallafa wa shugaban ƙasa a fannin yaɗa labarai da sadarwa.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Peter Obi Ya Gayyaci Gwamnan Bauchi Bala Abdulkadir Kan Yazo Su Hada Kai Su Gyara Nijeriya.
Next Post: Al’ummar Jihar Nasarawa Suna Cecekuce Bisa Tsaida Aliyu Wadada Takarar Gwamna

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Najeriya Tace Ta Farmaki Mayakan ISIS A Jihar Sokoto Labarai
Shugaba Trump Ya Bukaci Kasar Iran Ta Mika Wuya Amurka
Tattalin Arzikin Kasar Botswana Zai Farfado Afrika
Ukraine Ta Tura Tawagar Kwarerru Zuwa Kasashen Larabawan Domin Basu Kariya Labarai
Babban Sakataren MDD Yayi Allah Wadai Da Matakin Soja A Gabas Ta Tsakiya Afrika
Hanyar Gombe Dukku Darazo Ta Zamo Abun Damuwa Ga Al’ummar Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Iran Ta Bukaci Duniya Ta Shirya Domin Fuskantar Tsadan Mai Amurka
  • Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kama Muhyi Magaji Siyasa ce Kawai Inji Gwamnatin Kano Labarai
  • Yawan wadanda suka mutu a mummunan harin yanbindiga a Jihar kwaran Najeriya yakai 170 Najeriya
  • Ghana Ta Haramta Hakar Ma’adinai A Gandunan Dajin Data Kebe, Labarai
  • ‘Yan Sandan Jihar Bauchi Sun Kama Wasu Matasa da Ake Zargin Su Da Sara Suka  Labarai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Aikin Wutan Lantarki A Jami’ar Bayero Afrika
  • Harkar Zirga Zirgar Jiragen Sama Ya Bunkasa A Kenya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.