Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Soyinka Ya soki Yawan Jami’an Tsaron Da Ake Bai Wa Seyi Tinubu
Published: December 10, 2025 at 4:23 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Farfesa Wole Soyinka ya yi gargaɗi ga Shugaba Bola Tinubu kan yadda ake gudanar da tsaro da kuma amfani da jami’an gwamnati wajen kare wasu ‘yan tsiraru masu kusanci da fada.

Yayin bikin bayar da kyaututtuka na Wole Soyinka Centre for Investigative Journalism a Legas, a wani bidiyo da ya yadu, Soyinka ya ce ya yi mamakin ganin “babbar rundunar tsaro” da aka bai wa Seyi Tinubu, ɗan shugaban ƙasa, a Ikoyi.

Ya bayyana cewa yawan jami’an tsaron da ya gani “ya isa ya mamaye ƙaramar ƙasa,” lamarin da ya sa ya tuntubi mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, domin neman bayani.

Soyinka ya ce bai dace ‘ya’yan shugabanni su gaji karfin gwamnati ko su yi yawo da tsaro fiye da kima ba, yayin da ƙasar ke fama da hare-hare, garkuwa da mutane da rashin tsaro a sassa da dama.

Ya ƙara da cewa irin wadannan albarkatun tsaro ya fi dacewa a tura su wuraren da ake bukata, ba wajen kare masu gata ba.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami
Next Post: Shugaba Tinubu Ya Umarci Janye ‘Yan Sanda Masu Gadin Ministoci

Karin Labarai Masu Alaka

CBN: An Samu Ƙaruwar Masu Cin Bashin Banki Basa Biya Najeriya
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Hare Hare Daban Daban A Najeriya Najeriya
Kamfanin Mai Na NNPC Yasamu Gwaggwabar Riba Labarai
Tinubu Ya Yi Allah Wadai Da Kashe-kashen Jos Da Kaduna Afrika
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Katsina Afrika
Taron Masu Mu’amala Da Kafar Facebook A Kano Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kungiyar Maharba Da ‘Yan Sintiri Sun Samu Kyautar Motoci Labarai
  • Jam’iyar APC A Najeriya Ta Kaddamar Da Bada Shaidar Zama Dan Jam’iyyar Ta Na’ura Mai Kwakwalwa Siyasa
  • An Kara Wa’adin Zaman Kurkuku A Senegal Ga Masu Auren Jinsi Afrika
  • An Kashe Sojojin Bangladesh A Kasar Sudan Tsaro
  • Shugaban Mulkin Soja A Mali Ya Kirkiro Mukami Kamar Minista Afrika
  • Jami’in Diflomasiyyar Da Ake Zargi Da Kisan Prime minister Ya Daukaka Kara Afrika
  • Yeriman Ingila Ya Mayarwa Trump Martani Amurka
  • Pakistan Zata Karbi Bakwancin Saudiya, Turkiyya Da Masar Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.