Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar Gombe, CP Umar Ahmed Chuso, ya jaddada shirye-shiryen rundunar ‘yan sanda wajen magance munanan dabi’u a tsakanin matasa a fadin jihar.
Kwamishinan ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi a taron hulɗa da al’umma da wayar da kai kan yaƙi da munanan dabi’u ta hanyar aikin ‘yan sanda wanda aka gudanar a Gombe International Hotel.
Ya ƙara da cewa yana da tsare-tsare na ƙarfafa aikin ‘yan sanda na rigakafi ta hanyar haɗin gwiwa da shugabannin addinai, shugabannin al’umma da sarakunan gargajiya, da sauran masu ruwa da tsaki.
A saƙonnin fatan alheri, Shugaban ƙungiyar Kiristoci ta CAN a jihar Gombe, Reverend Joseph Alphonsus Shenga, da Shugaban Jama’atu Nasril Islam a jihar, Alhaji Saleh Danburam, tare da Ibrahim Yusuf 3000, sun ba da tabbacin goyon bayansu ga shirye-shiryen Kwamishinan ‘yan sanda na yaƙi da shan miyagun ƙwayoyi, daba, da kuma inganta tsaron al’umma ta hanyar aikin ‘yan sanda na rigakafi.
Sun kuma yaba da jajircewar Kwamishinan ‘yan sandan tare da kira ga samar da isassun jami’an tsaro a muhimman sassan jihar domin ƙarfafa ƙoƙarin yaƙi da rashin tsaro.
Da yake nasa jawabin, mai riƙe da sarautar Wazirin Yeriman Gombe, Alhaji Yaya Hammari, ya yi bayani kan tarihin aikin ‘yan sanda a jihar, inda ya yaba da ƙirƙirar wannan taro na hulɗa da al’umma wanda zai taimaka wajen rage munanan dabi’u.
Ya bayyana cewa shan kayan maye a tsakanin matasa na haddasa rashin aikin yi da sauran matsaloli a cikin al’umma, tare da kira ga bayar da cikakken goyon baya da haɗin kai domin samun nasara.
Shi ma Shugaban PCRC na jihar Gombe, Kwamared Garba Ubale, ya ce wannan shiri na Kwamishinan abin a yaba ne, yana mai cewa wannan shi ne karo na uku da aka gudanar a ƙarƙashin jagorancin CP Ahmed Chuso.
Ya kuma yaba da ƙoƙarin DPO na Pantami bisa fahimta da jajircewa, tare da kira da a ƙara ƙaimi wajen yaƙi da munanan dabi’u domin ci gaban al’umma.
A nasa ɓangaren, Abdulaziz Sani Labaran na Youth O’Clock, a cikin takardar da ya gabatar, ya bayyana cewa wasu ‘yan siyasa da wasu na taimakawa wajen jefa matasa cikin shan kayan maye, inda ya buƙaci a ɗauki matakan da za su kawo ƙarshen lamarin.
A takardar daya Gabatar Malami Daga Sashin ilimin halayyar Dan Adam na jami’ar jihar Gombe Dr. Ahmad Adamu ya bayyana aikin tsaro a matsayin Wani muhimmin aiki Wanda yake taimakawa Wajen kyautata rayuwar al’umma.
Dr. Ahmad Yace akwai kwarewa tare da salo ayyukan Jami’an Tsaro Wajen Kawo Karshen matsalar Tsaro a cikin al’umma, inda ya bukaci Samun hadinkan al’umma wajen Samun nasarar Abunda aka Saka a gaba.


