Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

‘Yan Sanda A Gombe Sun Jaddada Shirin Yaƙi Da Munanan Dabi’u
Published: May 4, 2026 at 11:03 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar Gombe, CP Umar Ahmed Chuso, ya jaddada shirye-shiryen rundunar ‘yan sanda wajen magance munanan dabi’u a tsakanin matasa a fadin jihar.

Kwamishinan ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi a taron hulɗa da al’umma da wayar da kai kan yaƙi da munanan dabi’u ta hanyar aikin ‘yan sanda wanda aka gudanar a Gombe International Hotel.

Ya ƙara da cewa yana da tsare-tsare na ƙarfafa aikin ‘yan sanda na rigakafi ta hanyar haɗin gwiwa da shugabannin addinai, shugabannin al’umma da sarakunan gargajiya, da sauran masu ruwa da tsaki.

A saƙonnin fatan alheri, Shugaban ƙungiyar Kiristoci ta CAN a jihar Gombe, Reverend Joseph Alphonsus Shenga, da Shugaban Jama’atu Nasril Islam a jihar, Alhaji Saleh Danburam, tare da Ibrahim Yusuf 3000, sun ba da tabbacin goyon bayansu ga shirye-shiryen Kwamishinan ‘yan sanda na yaƙi da shan miyagun ƙwayoyi, daba, da kuma inganta tsaron al’umma ta hanyar aikin ‘yan sanda na rigakafi.

Sun kuma yaba da jajircewar Kwamishinan ‘yan sandan tare da kira ga samar da isassun jami’an tsaro a muhimman sassan jihar domin ƙarfafa ƙoƙarin yaƙi da rashin tsaro.

Da yake nasa jawabin, mai riƙe da sarautar Wazirin Yeriman Gombe, Alhaji Yaya Hammari, ya yi bayani kan tarihin aikin ‘yan sanda a jihar, inda ya yaba da ƙirƙirar wannan taro na hulɗa da al’umma wanda zai taimaka wajen rage munanan dabi’u.

Ya bayyana cewa shan kayan maye a tsakanin matasa na haddasa rashin aikin yi da sauran matsaloli a cikin al’umma, tare da kira ga bayar da cikakken goyon baya da haɗin kai domin samun nasara.

Shi ma Shugaban PCRC na jihar Gombe, Kwamared Garba Ubale, ya ce wannan shiri na Kwamishinan abin a yaba ne, yana mai cewa wannan shi ne karo na uku da aka gudanar a ƙarƙashin jagorancin CP Ahmed Chuso.

Ya kuma yaba da ƙoƙarin DPO na Pantami bisa fahimta da jajircewa, tare da kira da a ƙara ƙaimi wajen yaƙi da munanan dabi’u domin ci gaban al’umma.

A nasa ɓangaren, Abdulaziz Sani Labaran na Youth O’Clock, a cikin takardar da ya gabatar, ya bayyana cewa wasu ‘yan siyasa da wasu na taimakawa wajen jefa matasa cikin shan kayan maye, inda ya buƙaci a ɗauki matakan da za su kawo ƙarshen lamarin.

A takardar daya Gabatar Malami Daga Sashin ilimin halayyar Dan Adam na jami’ar jihar Gombe Dr. Ahmad Adamu ya bayyana aikin tsaro a matsayin Wani muhimmin aiki Wanda yake taimakawa Wajen kyautata rayuwar al’umma.

Dr. Ahmad Yace akwai kwarewa tare da salo ayyukan Jami’an Tsaro Wajen Kawo Karshen matsalar Tsaro a cikin al’umma, inda ya bukaci Samun hadinkan al’umma wajen Samun nasarar Abunda aka Saka a gaba.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Sanata Goje Yayi Watsi Da Fidda ‘Yan Takarar APC A Gombe
Next Post: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Katsina

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamna Ododo Ya Gargadi Sarakunan Gargajiya Najeriya
‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 15 A Kasar Australiya Labarai
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Wajen Hakar Ma’adanai Dake Jihar Filato Najeriya
Mataimakin Shugaban Kasa Ya Sauka A Jihar Kwara Labarai
Amurka Zata Aika Jiragen Yaki Biyu Gabas Ta Tsakiya Amurka
Iran Zata Mayarwa Amurka Martani Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Alaka Na Cigaba Da Kamari Tsakanin Rwanda Da Barundi Labarai
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Kasar Netherland Ta Mayarwa Masar Mutum Mutumin Tarihi Afrika
  • Shugaba Tinubu: Naji Dadin Sako Daliban Neja Da Aka Sace Labarai
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028 Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Ta Jaddada Aniyarta Ta Daƙile Yaɗuwar Makamai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Afrika
  • Nigeria Zata Bude Asusun Dala Bilyan Biyu Don Habaka Sashin Makamashi Labarai
  • Ana Cigaba Da Kai Kayan Agaji Kasar Morocco Sakamakon Tsananin Hunturu Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.