Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Wani Jirgin Kasa Yayi Hatsari A Kudancin Spain
Published: January 19, 2026 at 8:58 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wani jirgin kasa mai saurin tafiya ya goce daga kan layin dogonsa ya kara tare da ture wani jirgin daban daga kan layinsa na dogo a yankin kudancin Spain, inda hukumomin ‘yan sanda suka tabbatar da cewa mutane akalla 21 sun mutu.

Wannan hatsarin ya faru ne a kusa da Adamuz a lardin Cordoba, inda gidan telebijin na kasar, Television Espanola, ya kara da cewa mutane 100 sun ji rauni, guda 25 daga cikinsu mummunan rauni.

Gidan telebijin na Espanola ya kara da cewa direban daya daga cikin jiragen wanda ya taso daga Madrid a kan hanyar zuwa Huelva, na daga cikin wadanda suka mutu.

Kamfanin dake tafiyar da layukan dogo na kasar, Adif, ya fada a wata sanarwar da ya bayar ta shafin sada zumunci cewa jirgin da ya fito daga Malaga a kan hanyar zuwa Madrid shine ya fara kauce ma layin dogonsa a Adamuz, ya fada kan daya layin dogon, ya kara da jirgin da ya taso daga Madrid a kan hanyar zuwa Huelva.

Kamfanin Adif yace hatsarin ya faru da karfe 6:40 na maraicen kasar, kimanin minti 10 bayan da jirgin farko ya bar Cordoba ya doshi Madrid.

Kamfanin Iryo, wanda ya mallaki jirgin kasan ya bayyana jimami da mummunan takaicin abinda ya faru, ya kuma kaddamar da shirinsa na gaggawa da yin aiki tare da hukumomin da abin ya shafa wajen tinkarar wannan lamari.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Senegal Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirka Afcon 2025.
Next Post: An Gano Wani Kurkukun Sirri Da Ake Azaftar Da Mutane A Kasar Libya

Karin Labarai Masu Alaka

Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya Afrika
Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin Afrika
Gwamnonin Arewa “Mun Amince Da Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
GoHealth Ta Buɗe Sabon Babin Kula Da Lafiya Ta Hanyar Fasaha Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Fara Wata Tattaunawa Afrika
  • Gidauniya: An Fara Tiyatar ‘Hernia’ Da ‘Hydrocele’ Kyauta A Jihar Katsina Labarai
  • Ministan Kudin Botswana Yace Akwai Hasashen Cewa Tattalin Arzikin Kasar Zai Ragu Amurka
  • Kungiyar ISIS Ta Kashe Sojojin Amurka Biyu Amurka
  • Kotu Ta Bada Belin Abubakar Malami Bisa Wasu Sharruda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Dubban ‘Yan Gudun Hijira Sun Halaka Amurka
  • Sakataren Gwamnatin Amurka Ya Bayyana Bawa Kungiyoyin Agaji Damar Kai Taimako Sudan Amurka
  • Hukumar MDD Tace Wadanda Suka Mutu A Harin Sudan Sun Haura 70 Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.