Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kungiyar ISIS Ta Kashe Sojojin Amurka Biyu
Published: December 13, 2025 at 7:55 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

An kashe sojojin Amurka biyu da wani farar hula ba Amurke daya, yayin da aka raunata wasu mutanen uku a lokacin da wani dan kungiyar ISIS yayi musu kwanton bauna ya bude musu wuta a yankin tsakiyar kasar Sham, watau Syria a yau din nan.

Wannan shine harin farko da ya haddasa mutuwa da aka kai kan sojojin Amurka a kasar ta Sham tun daga lokacin da aka hambarar da gwamnatin Shugaba Bashar al Assad shekara guda da ta shige.

Rundunar sojojin Amurka a yankin gabas ta tsakiya ta ce domin mutunta ‘yan’uwan mamatan, ba zata bayyana sunayensu ba har sai bayan sa’oi 24 da sanar da su.

Sakataren tsaron Amurka, Pete Hegseth, ya rubuta a shafin X cewa duk wanda ya kai hari ya kashe Amurkawa a ko ina yake a duniya, zai shafe sauran ‘yan kwanaki kalilan da suka rage masa a duniya da sanin cewa Amurka zata farauto shi, ta hallaka shi.

Kamfanin dillancin labarai na kasar Sham, SANA, ya fada tun farko cewa wannan harin da aka kai a kusa da kangon birni mai tarihi na zamanin da da ake kira Tadmur, ko Palmyra a turance, yayi sanadin raunata wasu sojojin Sham guda biyu da wasu na Amurka da dama.

SANA yace an kashe maharin ba tare da ba da karin bayani ba amma kungiyar sa’ido kan al’amuran kare hakkin bil Adama a Sham mai hedkwata a Britaniya, ta ce maharin sojan kasar Sham ne.

Amurka tana da daruruwan sojojin da ta girka a gabashin kasar Sham a wani bangare na gamayyar yaki da ‘yan ISIS

Amurka

Post navigation

Previous Post: Alhassan Yayi Nasarar Kifar Da Wurkilili A Gasar Damben Gargajiya
Next Post: Amurka Na Zargi Kasar Rwanda Da Kokarin Saba Yarjejeniyar Zaman Lafiya

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka Afrika
Amurka Ta Yi Juyin Mulki A Kasar Venezuela Amurka
Akwai Yiwuwar Iran Da Amurka Su Cimma Matsayar Dakatar Da Shirin Nukiliya Amurka
Yeriman Ingila Ya Gana Da Yeriman Saudiya Mai Jiran Gado Amurka
Kasashen Yankin Gulf Sun Bukaci Amurka Takawo Karshen Iran Afrika
Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Najeriya Bola Tinubu Zai Ziyarci Jihohin Borno,Bauchi Da Legas Labarai
  • Alhassan Yayi Nasarar Kifar Da Wurkilili A Gasar Damben Gargajiya Wasanni
  • Wasu Muhimman Abubuwa Da Najeriya Ba Zata Manta Da Su Ba A 2025 Labarai
  • Shugaba Tinubu: Naji Dadin Sako Daliban Neja Da Aka Sace Labarai
  • Amurka Zata Bada Gudumawar Kudi Dala Bilyan 10 Ga Ayyukan Kwamitin Wanzar Da Zaman Lafiyan Amurka
  • Kimanin Ganga Miliyan 40 Na Danyen Albarkatun Mai Yayi Kwantai A Kasashen Afirka Ta Yamma Afrika
  • Amurka Da Iran Zasu Tattauna A Kasar Oman Amurka
  • Gwamnan Gombe Ya kori Wasu Hadimansa Bisa Cin Zarafin Kansila Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.