Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Kungiyar ISIS Ta Kashe Sojojin Amurka Biyu
Published: December 13, 2025 at 7:55 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

An kashe sojojin Amurka biyu da wani farar hula ba Amurke daya, yayin da aka raunata wasu mutanen uku a lokacin da wani dan kungiyar ISIS yayi musu kwanton bauna ya bude musu wuta a yankin tsakiyar kasar Sham, watau Syria a yau din nan.

Wannan shine harin farko da ya haddasa mutuwa da aka kai kan sojojin Amurka a kasar ta Sham tun daga lokacin da aka hambarar da gwamnatin Shugaba Bashar al Assad shekara guda da ta shige.

Rundunar sojojin Amurka a yankin gabas ta tsakiya ta ce domin mutunta ‘yan’uwan mamatan, ba zata bayyana sunayensu ba har sai bayan sa’oi 24 da sanar da su.

Sakataren tsaron Amurka, Pete Hegseth, ya rubuta a shafin X cewa duk wanda ya kai hari ya kashe Amurkawa a ko ina yake a duniya, zai shafe sauran ‘yan kwanaki kalilan da suka rage masa a duniya da sanin cewa Amurka zata farauto shi, ta hallaka shi.

Kamfanin dillancin labarai na kasar Sham, SANA, ya fada tun farko cewa wannan harin da aka kai a kusa da kangon birni mai tarihi na zamanin da da ake kira Tadmur, ko Palmyra a turance, yayi sanadin raunata wasu sojojin Sham guda biyu da wasu na Amurka da dama.

SANA yace an kashe maharin ba tare da ba da karin bayani ba amma kungiyar sa’ido kan al’amuran kare hakkin bil Adama a Sham mai hedkwata a Britaniya, ta ce maharin sojan kasar Sham ne.

Amurka tana da daruruwan sojojin da ta girka a gabashin kasar Sham a wani bangare na gamayyar yaki da ‘yan ISIS

Amurka

Post navigation

Previous Post: Alhassan Yayi Nasarar Kifar Da Wurkilili A Gasar Damben Gargajiya
Next Post: Amurka Na Zargi Kasar Rwanda Da Kokarin Saba Yarjejeniyar Zaman Lafiya

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Majalisar Tarayyar Turai Yace Rasha Tana Cin Ribar Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
Afirka Ta Kudu Tace Bazata Yanke Alaka Da Iran Ba Afrika
Iran Zata Mayarwa Amurka Martanin Harin Kharg Afrika
Akwai Bukatar Nazari Game Da Dangantakar Iran Da Kasashen Gulf Amurka
‘Yan Kasar Venuzuela Zasu Fara Komawa Gida Amurka
Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jakadan Amurka A Poland Ya Yanke Hulda Da Kakakin Majalisar Kasar Labarai
  • Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Yayi Ajalin ‘Yan Ghana 50 Afrika
  • Shugaba Donald Trump Ya Nada Shugaban Bankin Tarayya Amurka
  • Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Zata Tabbatar Da Tsagaita Wuta A Kwango Afrika
  • Bayan Ya Ziyarci Kwankwaso Gawuna Zai Karbi Katin ADC Afrika
  • Magoya Bayan Dan Hamayya A Afirka Ta Kudu Sun Hallara A Kotu Afrika
  • Kauran Gwandu Zai Inganta Wutan Lantarki A Kebbi Siyasa
  • Barau Jibril: Mu Ba ‘Yan Amshin Shata Bane A Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.