Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin
Published: July 10, 2026 at 9:49 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin jihohin Arewacin Najeriya kuma Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ƙaddamar da sakatariyar wucin gadi ta ƙungiyar a birnin Kaduna, tare da yin kira ga shugabannin Arewa da su ƙara haɗa kai domin magance matsalolin tsaro, tattalin arziki da ci gaban da yankin ke fuskanta.

An ƙaddamar da sakatariyar ne a gini mai lamba 26 da ke kan titin Muhammadu Buhari Way, tsohuwar WAFF Road, inda kuma aka miƙa motocin aiki domin sauƙaƙa gudanar da ayyukan ƙungiyar.

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana cewa kafa sakatariyar wani muhimmin mataki ne na ƙarfafa ayyukan ƙungiyar da samar da ingantaccen tsari na daidaita manufofi da shirye-shiryen ci gaban jihohin Arewa 19.

Ya ce lokaci ya yi da shugabannin Arewa za su gina kan kyawawan tubalan da magabatan yankin suka kafa, tare da nuna jajircewa da sadaukarwa wajen magance ƙalubalen da yankin ke fuskanta.

Gwamnan ya jaddada cewa halin da Arewa ke ciki na buƙatar haɗin kai da ɗaukar matakai cikin gaggawa, yana mai bayyana cewa aiwatar da tsare-tsaren da ƙungiyar ta tsara zai taimaka wajen shawo kan matsalolin yankin.

A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Kebbi, Kwamared Nasir Idris, ya sake tabbatar da aniyar gwamnonin Arewa na ci gaba da haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen tunkarar matsalolin yankin. Ya kuma yabawa Gwamna Inuwa Yahaya bisa jagorancinsa wanda ya haifar da kafa sakatariyar ƙungiyar.

Shi ma Babban Daraktan Ƙungiyar Gwamnonin Arewa, Dakta Ezekiel Gomos, ya ce sabuwar sakatariyar za ta inganta gudanar da ayyuka, daidaita manufofi da shirye-shiryen ƙungiyar, tare da ƙara inganta haɗin gwiwa tsakanin ƙungiyar da sauran hukumomin yankin da na ƙasa.

Ya gode wa Gwamna Inuwa Yahaya da sauran gwamnonin Arewa bisa goyon bayan da suka bayar, yana mai tabbatar da cewa za a yi amfani da sakatariyar da motocin aikin cikin gaskiya da inganci domin cimma manufofin ƙungiyar.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya, Siyasa, Tsaro

Post navigation

Previous Post: TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta
Next Post: APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027

Karin Labarai Masu Alaka

Rundunar Operation Endurance Peace Ta Gano Wajen Kera Makamai A Jihar Filato Afrika
Shugaba Tinubu Zai Kara Karbo Bashin Dala Miliyan 516 Afrika
An Kashe Mayakan Sakai 67 A Pakistan Sauran Duniya
Gwamnonin Arewa “Mun Amince Da Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
Zargin Fitar Da Bayanan Masu Zabe A Najeriya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasashen Mali Da Burkina Faso Sun Haramtawa Amurkawa Shiga Kasashen Afrika
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe ‘Yan Sanda A Jihar Katsina Najeriya
  • An Bukaci Matasa Su Taka Gagarumar Rawa Wajen Gina Zaman Lafiya A Arewa Maso Gabas Afrika
  • Jagoran Addinin Kirista A Kaduna Ya Rabawa Fiye Da Musulmai Dubu Kayan Abincin Azumi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • EU Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Amurka Da Iran Afrika
  • Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC Najeriya
  • Matsalolin Masarautun Kano Sun Kawo Karshe Najeriya
  • Jami’an Tsaro Sun Dakile Safarar Makamai Daga Jos Zuwa Jihar Neja Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.