Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin jihohin Arewacin Najeriya kuma Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ƙaddamar da sakatariyar wucin gadi ta ƙungiyar a birnin Kaduna, tare da yin kira ga shugabannin Arewa da su ƙara haɗa kai domin magance matsalolin tsaro, tattalin arziki da ci gaban da yankin ke fuskanta.

An ƙaddamar da sakatariyar ne a gini mai lamba 26 da ke kan titin Muhammadu Buhari Way, tsohuwar WAFF Road, inda kuma aka miƙa motocin aiki domin sauƙaƙa gudanar da ayyukan ƙungiyar.
Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana cewa kafa sakatariyar wani muhimmin mataki ne na ƙarfafa ayyukan ƙungiyar da samar da ingantaccen tsari na daidaita manufofi da shirye-shiryen ci gaban jihohin Arewa 19.
Ya ce lokaci ya yi da shugabannin Arewa za su gina kan kyawawan tubalan da magabatan yankin suka kafa, tare da nuna jajircewa da sadaukarwa wajen magance ƙalubalen da yankin ke fuskanta.
Gwamnan ya jaddada cewa halin da Arewa ke ciki na buƙatar haɗin kai da ɗaukar matakai cikin gaggawa, yana mai bayyana cewa aiwatar da tsare-tsaren da ƙungiyar ta tsara zai taimaka wajen shawo kan matsalolin yankin.

A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Kebbi, Kwamared Nasir Idris, ya sake tabbatar da aniyar gwamnonin Arewa na ci gaba da haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen tunkarar matsalolin yankin. Ya kuma yabawa Gwamna Inuwa Yahaya bisa jagorancinsa wanda ya haifar da kafa sakatariyar ƙungiyar.
Shi ma Babban Daraktan Ƙungiyar Gwamnonin Arewa, Dakta Ezekiel Gomos, ya ce sabuwar sakatariyar za ta inganta gudanar da ayyuka, daidaita manufofi da shirye-shiryen ƙungiyar, tare da ƙara inganta haɗin gwiwa tsakanin ƙungiyar da sauran hukumomin yankin da na ƙasa.
Ya gode wa Gwamna Inuwa Yahaya da sauran gwamnonin Arewa bisa goyon bayan da suka bayar, yana mai tabbatar da cewa za a yi amfani da sakatariyar da motocin aikin cikin gaskiya da inganci domin cimma manufofin ƙungiyar.


