Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin jihohin Arewa (NSGF) kuma Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, ya yi Allah wadai da harin da aka kai Angwan Rukuba dake Ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa a Jihar Filato, yana mai bayyana lamarin a matsayin abin takaici, abin zargi kuma wadda ya yi hannun riga da kyawawan ɗabi’un Arewacin Najeriya.
Da yake tsokaci martani jim kaɗan bayan kammala taron shekara-shekara na ƙungiyar da aka gudanar a masauƙin Gwamnan jihar Gombe dake Abuja, Gwamna Inuwa Yahaya yace gwamnonin sun kammala wata bita mai zurfi kan sha’anin tsaro a faɗin Arewa, inda suka sabunta ƙudurinsu na fuskantar ƙalubalen tsaro da tattalin arziki dake fuskantar al’ummar yankin.
Yace abin takaicin da ya faru a Jihar Filato ya ƙara ƙarfafa himmatuwar Ƙungiyar na tabbatar da zaman lafiya, tsaro da kuma yin haɗin gwiwa mai ƙarfi da hukumomin tsaro.
Shugaban ƙungiyar ya jaddada cewa irin waɗannan aika-aikan tashin hankali baƙon abu ne ga Arewa, yankin da aka san shi da zaman tare, girmama juna da ‘yan’uwantaka mai ɗorewa tsakanin al’ummomi daban-daban.
Gwamna Inuwa Yahaya ya yi ƙira ga al’ummar Jihar Filato, musamman waɗanda ke cikin yankin da abin ya shafa, su kwantar da hankalinsu su guji ɗaukar doka a hannunsu. Ya yi gargaɗin cewa ɗaukar fansa da kuma ɗaukar matakin tayar da hankali na iya ƙara ta’azzara yanayin da ya riga ya ƙazance.
Ya buƙaci shugabannin al’umma, malaman addini, kungiyoyin matasa, da duk masu ruwa da tsaki su yi aiki tare don samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.
Gwamna Inuwa Yahaya ya kuma yabawa Gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang, saboda matakan gaggawa da ya ɗauka don daƙile lamarin, musamman sanya dokar hana fita ta awanni 48 a Ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa da kuma tura jami’an tsaro cikin gaggawa don dawo da doka da oda.
A cewarsa, matakan da Gwamnatin jihar Filato ta ɗauka sun nuna kyakkyawan jagoranci wajen kare rayuka da kuma daƙile ci gaba da faɗaɗar rikicin.
“Ina yabawa ɗan’uwana gwamna mai girma Caleb Mutfwang, bisa matakan gaggawa da ya ɗauka don shawo kan lamarin da kuma dawo da kwanciyar hankali. Waɗannan matakai sun dace kuma suna da matuƙar muhimmanci wajen daƙile taɓarɓarewar doka da oda,” in ji shi.
Gwamnan na Gombe ya sake jaddada ƙudurin gwamnonin Arewa na ci gaba da baiwa rundunonin tsaro da sauran hukumomi tallafin da ya dace don sauƙe nauyin dake kansu na kundin tsarin mulki.
Yace kan ƙungiyar a haɗe yake kan ƙudurinta na ƙarfafa haɗin gwiwa don yaƙi da laifuka, tashin hankali da duk wata barazana ga zaman lafiya.
Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana ƙwarin gwiwar cewa za a kamo waɗanda suka kai harin kuma a gurfanar da su gaban kuliya, yayin da yake miƙa ta’aziyya ga gwamnati da al’ummar Jihar Filato, musamman iyalan da suka rasa ‘yan uwa a cikin wannan bala’i.
Ya yi addu’ar Allah ya jiƙan waɗanda suka mutu, ya kuma yi fatan samun sauki cikin gaggawa ga waɗanda suka jikkata


