Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika

Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Harin Jos
Published: March 31, 2026 at 11:38 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin jihohin Arewa (NSGF) kuma Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, ya yi Allah wadai da harin da aka kai Angwan Rukuba dake Ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa a Jihar Filato, yana mai bayyana lamarin a matsayin abin takaici, abin zargi kuma wadda ya yi hannun riga da kyawawan ɗabi’un Arewacin Najeriya.

Da yake tsokaci martani jim kaɗan bayan kammala taron shekara-shekara na ƙungiyar da aka gudanar a masauƙin Gwamnan jihar Gombe dake Abuja, Gwamna Inuwa Yahaya yace gwamnonin sun kammala wata bita mai zurfi kan sha’anin tsaro a faɗin Arewa, inda suka sabunta ƙudurinsu na fuskantar ƙalubalen tsaro da tattalin arziki dake fuskantar al’ummar yankin.

Yace abin takaicin da ya faru a Jihar Filato ya ƙara ƙarfafa himmatuwar Ƙungiyar na tabbatar da zaman lafiya, tsaro da kuma yin haɗin gwiwa mai ƙarfi da hukumomin tsaro.

Shugaban ƙungiyar ya jaddada cewa irin waɗannan aika-aikan tashin hankali baƙon abu ne ga Arewa, yankin da aka san shi da zaman tare, girmama juna da ‘yan’uwantaka mai ɗorewa tsakanin al’ummomi daban-daban.

Gwamna Inuwa Yahaya ya yi ƙira ga al’ummar Jihar Filato, musamman waɗanda ke cikin yankin da abin ya shafa, su kwantar da hankalinsu su guji ɗaukar doka a hannunsu. Ya yi gargaɗin cewa ɗaukar fansa da kuma ɗaukar matakin tayar da hankali na iya ƙara ta’azzara yanayin da ya riga ya ƙazance.

Ya buƙaci shugabannin al’umma, malaman addini, kungiyoyin matasa, da duk masu ruwa da tsaki su yi aiki tare don samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Gwamna Inuwa Yahaya ya kuma yabawa Gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang, saboda matakan gaggawa da ya ɗauka don daƙile lamarin, musamman sanya dokar hana fita ta awanni 48 a Ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa da kuma tura jami’an tsaro cikin gaggawa don dawo da doka da oda.

A cewarsa, matakan da Gwamnatin jihar Filato ta ɗauka sun nuna kyakkyawan jagoranci wajen kare rayuka da kuma daƙile ci gaba da faɗaɗar rikicin.

“Ina yabawa ɗan’uwana gwamna mai girma Caleb Mutfwang, bisa matakan gaggawa da ya ɗauka don shawo kan lamarin da kuma dawo da kwanciyar hankali. Waɗannan matakai sun dace kuma suna da matuƙar muhimmanci wajen daƙile taɓarɓarewar doka da oda,” in ji shi.

Gwamnan na Gombe ya sake jaddada ƙudurin gwamnonin Arewa na ci gaba da baiwa rundunonin tsaro da sauran hukumomi tallafin da ya dace don sauƙe nauyin dake kansu na kundin tsarin mulki.

Yace kan ƙungiyar a haɗe yake kan ƙudurinta na ƙarfafa haɗin gwiwa don yaƙi da laifuka, tashin hankali da duk wata barazana ga zaman lafiya.

Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana ƙwarin gwiwar cewa za a kamo waɗanda suka kai harin kuma a gurfanar da su gaban kuliya, yayin da yake miƙa ta’aziyya ga gwamnati da al’ummar Jihar Filato, musamman iyalan da suka rasa ‘yan uwa a cikin wannan bala’i.

Ya yi addu’ar Allah ya jiƙan waɗanda suka mutu, ya kuma yi fatan samun sauki cikin gaggawa ga waɗanda suka jikkata

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Bayan Ya Ziyarci Kwankwaso Gawuna Zai Karbi Katin ADC
Next Post: Yusuf Gawuna Ya Koma Jam’iyar ADC

Karin Labarai Masu Alaka

Malami: Gwamnatin APC Ta Gaza – “Yan-Kasa Kuwa Na Da Katin Zabe” Labarai
Hukumar Ƴan Sanda Ta Musanta Zargin Kashe Ɗan Achaba a Gombe Tsaro
Na Yi Murabus Ne Don Amurka Ta Keta Haddin Iraniyawa Amurka
Libya Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashen Faransa Da Amurka Afrika
Tinubu: Sojojin Mu Sun Yi Rawar Gani Don Kare Demokuraɗiyya A Jamhuriyar Binin Labarai
An Zargi Babban Mai Gabatar Da Kara A Kotun Duniya Ta ICC Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Farashin Mai A Kasuwannin Duniya Yayi ƙasa Kadan Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Kasar Madagascar Ya Kori Prime Minista Da ‘Yan Majalisa Afrika
  • Afirka Ta Kudu Tace Bazata Yanke Alaka Da Iran Ba Afrika
  • ‘Yan Sandan Habasha Sun Kama Dubban Albarusai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Juma’a 11.21.2025 Rediyo
  • Sanata Goje Yayi Watsi Da Fidda ‘Yan Takarar APC A Gombe Afrika
  • Zaizayar Kasa Tayi Ajalin Mutane 200 A Kasar Congo Afrika
  • Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.