Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

An tura tsohon ministan Ilimin Nijar gidan yari saboda zargin aikata fyade ga wata daliba.
Published: January 8, 2026 at 1:38 PM | By: Mustapha Nasiru Batsari | Updated: January 8, 2026

Hukumomi a Jamhuriyar Nijar sun cafke tsofon ministan ilimi mai zurfi PhD Mamadou Djibo sakamakon zargin yi wa wata daliba fyade. Tuni a ka wuce da shi gidan yari a ci gaba da binciken wannan al’amari da ta farfado da mahawwara game da cin zarafi mata a makarantu.
Wakilin GTA Hausa Amurka ke Magana Souley Moumouni Barma ya aiko mana Karin bayani daga birnin Yamai.
Ainahi tsofon minista Mamodou Djibo ya gurfana a ofishin ‘yan sandan farin kaya inda aka saurare shi bayan da wata daliba ta shigar da kara a bisa zarginsa da yi ma ta fyade. Daga bisani maganar ta kara gaba zuwa kotu inda alkali mai tuhuma ya damka shi a hannun alkali mai bincike wanne ya tura shi gidan yarin Kollo a ci gaba da bincike. abinda ‘yan kasa ke ganin alama ce ta yunkurin zartas da abubuwan da dokokin kasa suka yi tanadi dangane da batun cin zarafin mata. Alhaji Abdou Maman Lokoko na daga cikin shugabanin kungiyoyin bunkasa ilimi a Nijar.

Majiyoyi na cewa dalibar da ta bankado wannan badakala na daga cikin daliban makarantar da ke karatu a makarantar tsofon minista PhD Mamadou Djibo lamarin da ke farfado da mahawwara game da yanayin da dalibai mata ke karatu cikinsa. Wata ‘yar fafutika Housseina Maizoumbou na ganin lokaci ya yi da za a kawo karshen matsalar.

A nan gaba ne a ke saran gurfanar da tsohon ministan na ilimi a gaban alkali domin tantance zahirin abubuwan da suka faru.
Dan rajin kare hakkin dan adam Abdourahamane Oumarou na cewa…

Kawo yanzu ba wani takamemen bayani daga bangaren mashara’anta haka kuma wani makusancin ministan da ke zargi ko laiyansa ba su ce kala ba game da wannan dambarwa.

An tura tsohon ministan Ilimin Nijar gidan yari saboda zargin aikata fyade.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/01/TSOHON-MINISTA-NIJAR.mp3
Afrika

Post navigation

Previous Post: Amurka Ta Kama Tsohon Ministan Kudin Kasar Ghana
Next Post: Sarkin Kagarko Ya Rasu Yana Da Shekaru 110

Karin Labarai Masu Alaka

Ana Kokarin Kawo Karshen Matsalar Kashe Matafiya A Filato Afrika
Rasha Ta Gargadi Amurka Da Isra’ila Kan Harin Iran Afrika
Iran Ta Karyata Tattaunawa Da Washington Afrika
Afirka Ta Kudu Ta Bayyana Yadda Aka Yaudari ‘Yan Kasar Ake Tilasta Musu Ayyukan Bauta Afrika
Sarkin Musulmi Ya Ziyarci Shugaba Bola Tinubu Afrika
An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jami’an Shiga Da Fice A Afirka Ta Kudu Sun Tafka Badakalar Kudade Afrika
  • Bankin Duniya Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Afirka Da Yankin Sahara Afrika
  • Jami’an tsaro sama da dubu biyar ne zasuyi aikin tabbatar da tsaro Alokacin bikin karamar sallah a Jihar Nejan Najeriya. Najeriya
  • Shugaba Trump Da Gwamnan Minnesota Zasu Sassautawa Bakin Haure Amurka
  • Majalisar Dattawan Amurka Ta Amince Da Wata Doka Amurka
  • Kwankwaso: Gwamnatin Kano Tamuce Baki Daya, Tafiya APC Allah Ya Raka Taki Gona! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Ta Tallafa Wa ’Yan Sanda Da Motoci Afrika
  • Harin ‘Yan Daba Ya Hallaka Mutane 70 A Kasar Haiti Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.