
SAMA DA JAMI’AN TSARO DUBU BIYAR ZASUYI AIKIN BADA KARIYA ALOKACIN BIKIN KARAMAR SALLAH A JIHAR NEJAN NAJERIYA.
Kimanin Jami,an tsaro dubu biyar ne zasuyi aikin sanya idanu domin tabbatar da bukukuwan karamar Sallah lafiya a Jihar Nejan Najeriya,
Rundunar Yansanda ta Jihar Nejan dai tace sun dauki tsauraran Matakai na sanya Idanu a Masallatan idi dake sassan Jihar domin magance duk wata barazana da zata hadari ga Lafiya Al,umma,
Jihar Neja dai na daya daga cikin jihohin Arewacin Najeriya dake fama da Matsalar rashin tsaron Kwamishinan Yansanda na Jihar Nejan CP Adamu Elleman ya shedawa manema labarai cewa suna aiki kafada da kafada da Sauran Jami,an tsaro domin samun Nasarar yaki da bata gari…
Wannan Mataki na Jami,an tsaron a Jihar Neja Yana zuwa ne Kwana daya bayan tashin wasu bama bamai a Jihar Borno lamarin da Kwamishinan yansandan Jihar Nejan yace ya kara zaburar dasu…
Ahalin da ake ciki dai rundunar Yansanda Jihar Nejan ta haramta buga na,urar nan mai kara da ake kira Nuk out Alokacin bukukuwan karamar Sallah,sannan ta Umurni mazauna yankunan karkara a bangaren Borgu da Agwara da Kuma Kontagora da su shiga cikin Manyan Garuruwan dake kusa dasu domin Gudanar da bukukuwan su na Wannan karamar Sallah Mai domin baiwa kansu kariya daga miyagu.
” »

