Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Majalisar Tarayya Ta Amince Da Gyara Dokar Kasafin Kudi
Published: December 24, 2025 at 7:57 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

A karon farko a tarihin Najeriya, Majalisar Dokokin Kasa ta amince wa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu yin aiki da kasafin kudin shekara 2024 da na 2025 har zuwa watan Maris na shekara 2026 mai zuwa.

Wakiliyar GTA Hausa Medina Dauda ta hada mana rahoto kan dalilan da ya sa Majalisar ta aiwatar da wannan aiki, Majalisar Dattawa da ta Wakilai sun amince da gyara kudurin dokar kasafin kudin shekara 2024 da ta 2025 inda aka dunkule kashi 70 na kudaden manyan aiyukan wadannan shekaru har zuwa watan Maris na shekara 2026 inda ake fatan kammala dukkan aiyukan a cikin lokaci kana a fara aiki da kasafin kudin shekara 2026 daga watan Afrilu.

Yan Majalisar sun goyi bayan kudurin wanda aka karanta kuma aka zartar da shi ta hanyar karatu na farko da na biyu da na uku a zama daya kamar yadda Shugaban Kwamitin Kasafin Kudi na Majalisar Dattawa Sanata Solomon Adeola Olamilekan ya baiyana mana bayan sun kammala zaman a jiya talata.

Olamilekan ya ce ana bukatar karin lokaci don baiwa Gwamnatin Taraiyya damar Kammala wasu aiyuka da ake ci gaba da yi a karkashin Kasafin kudin shekara 2025.

Olamilekan ya ce an yi wannan tsawaitawan ne saboda Najeriya za ta cigaba da gudanar da kasafin kudi guda daya rak daga watan Afrilun badi don inganta amfani da kudaden da aka ware da kuma ba da damar kammala muhimman aiyukan samar da ababen more rayuwa.

A bangaren Majalisar Wakilai kuma Dan Majalisa Daga Jihar Jigawa Abubakar Hassan Fulata yayi bayanin dalilin da ya sa Majalisa ta dauki wannan mataki na tsawaita Kasafin Kudin shekra 2924 da na 2025 din cikin gaggawa Majalisa ta tafi hutun karshen shekara sai ranan 27 ga watan Janairu na shekara 2026 za su dawo bakin aiki.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Jihar Ekiti Ta Aiwatar Da Dokar Haraji
Next Post: Anyi Rashin Mutane Da Yawa Yayinda Bom Ya Fashe Ana Sallar Magariba Maiduguri

Karin Labarai Masu Alaka

An Gudanar Da Addu’o’i Na Musamman Don Neman Zaman Lafiya Labarai
Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela Amurka
Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Haifar Da Tsadar Taki Da Mai Ga Manoma Labarai
Kungiyar Mata Manoma A Najeriya Ta Raba Kyautar Abinci A Gombe Afrika
Shugaban Ƙasar China Zai Karbi Bakwancin Shugaban Koriya Ta Kudu Afrika
‘Yan Sandan Jihar Bauchi Sun Kama Wasu Matasa da Ake Zargin Su Da Sara Suka  Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe
  • An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe 
  • Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi
  • Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Wikki Tourist FC: Ta Sallami ‘Yan Wasa Hudu Wasanni
  • Shugaban Kasar Uganda Yana Kokarin Mayar Da Mulkin Kasar Na Gado Labarai
  • Baitul Malin Amurka Zata Bawa Venezuela Da Cuba Damar Sayar Da Mai Amurka
  • Ba Mamaki APC Ta Kafa Tarihi A Ranar Litinin Najeriya
  • Motsepe, Daga 2028 AFCON Zata Sauya Daga Shekaru Biyu Zuwa Hudu Wasanni
  • Sama Da Zawiyya 100 Ne Suka Samu Tallafin Kayan Abinci Daga Al’mustapha Haji Sufi Labarai
  • Fitaccen Dan Jarida a Sokoto Surajo Dalhatu Sifawa Ya Rasu Najeriya
  • Zelensky Na Buƙatar Ganawa Da Trump Domin Cimma Matsaya Kan Batutuwa Masu Sarƙaƙiya Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.