Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Majalisar Tarayya Ta Amince Da Gyara Dokar Kasafin Kudi
Published: December 24, 2025 at 7:57 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

A karon farko a tarihin Najeriya, Majalisar Dokokin Kasa ta amince wa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu yin aiki da kasafin kudin shekara 2024 da na 2025 har zuwa watan Maris na shekara 2026 mai zuwa.

Wakiliyar GTA Hausa Medina Dauda ta hada mana rahoto kan dalilan da ya sa Majalisar ta aiwatar da wannan aiki, Majalisar Dattawa da ta Wakilai sun amince da gyara kudurin dokar kasafin kudin shekara 2024 da ta 2025 inda aka dunkule kashi 70 na kudaden manyan aiyukan wadannan shekaru har zuwa watan Maris na shekara 2026 inda ake fatan kammala dukkan aiyukan a cikin lokaci kana a fara aiki da kasafin kudin shekara 2026 daga watan Afrilu.

Yan Majalisar sun goyi bayan kudurin wanda aka karanta kuma aka zartar da shi ta hanyar karatu na farko da na biyu da na uku a zama daya kamar yadda Shugaban Kwamitin Kasafin Kudi na Majalisar Dattawa Sanata Solomon Adeola Olamilekan ya baiyana mana bayan sun kammala zaman a jiya talata.

Olamilekan ya ce ana bukatar karin lokaci don baiwa Gwamnatin Taraiyya damar Kammala wasu aiyuka da ake ci gaba da yi a karkashin Kasafin kudin shekara 2025.

Olamilekan ya ce an yi wannan tsawaitawan ne saboda Najeriya za ta cigaba da gudanar da kasafin kudi guda daya rak daga watan Afrilun badi don inganta amfani da kudaden da aka ware da kuma ba da damar kammala muhimman aiyukan samar da ababen more rayuwa.

A bangaren Majalisar Wakilai kuma Dan Majalisa Daga Jihar Jigawa Abubakar Hassan Fulata yayi bayanin dalilin da ya sa Majalisa ta dauki wannan mataki na tsawaita Kasafin Kudin shekra 2924 da na 2025 din cikin gaggawa Majalisa ta tafi hutun karshen shekara sai ranan 27 ga watan Janairu na shekara 2026 za su dawo bakin aiki.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Jihar Ekiti Ta Aiwatar Da Dokar Haraji
Next Post: Anyi Rashin Mutane Da Yawa Yayinda Bom Ya Fashe Ana Sallar Magariba Maiduguri

Karin Labarai Masu Alaka

Tattalin Arzikin Najeriya Ya Farfardo Bisa Samun Wasu Sauye Sauye Labarai
Nuhu Ribadu Ya Mika Dalibai 100 da Aka Ceto Ga Gwamnatin Jihar Neja Labarai
Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura Labarai
Gwannatin Jihar Kebbi Ta Arawa Maniyyata Kuɗin Aikin Hajji 2026, Labarai
Ganduje Ya Nisanta Kansa Da Batan Dadiyata Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Farashin Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Labarai
  • Hukumar DSS Ta Sake Kama Abubakar Malami Labarai
  • Sanata Barau Ya Raba Motoci Da Babura Ga Al’ummar Kano Ta Arewa Afrika
  • NUT Ta Shiga Yajin Aikin Sai Baba Ta Gani Afrika
  • Wata Mace Ta Mutu A Hannun ‘Yan-Fashin Daji, Wata Ta Haihu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Manchester United: Za Ta Nada Michael Carrick A Matsayin Kocin Riƙon ƙwarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mun Kwato Kimanin Naira Biliyan 40 Na Badakala A Tsawon Shekara Daya Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.