Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Majalisar Tarayya Ta Amince Da Gyara Dokar Kasafin Kudi
Published: December 24, 2025 at 7:57 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

A karon farko a tarihin Najeriya, Majalisar Dokokin Kasa ta amince wa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu yin aiki da kasafin kudin shekara 2024 da na 2025 har zuwa watan Maris na shekara 2026 mai zuwa.

Wakiliyar GTA Hausa Medina Dauda ta hada mana rahoto kan dalilan da ya sa Majalisar ta aiwatar da wannan aiki, Majalisar Dattawa da ta Wakilai sun amince da gyara kudurin dokar kasafin kudin shekara 2024 da ta 2025 inda aka dunkule kashi 70 na kudaden manyan aiyukan wadannan shekaru har zuwa watan Maris na shekara 2026 inda ake fatan kammala dukkan aiyukan a cikin lokaci kana a fara aiki da kasafin kudin shekara 2026 daga watan Afrilu.

Yan Majalisar sun goyi bayan kudurin wanda aka karanta kuma aka zartar da shi ta hanyar karatu na farko da na biyu da na uku a zama daya kamar yadda Shugaban Kwamitin Kasafin Kudi na Majalisar Dattawa Sanata Solomon Adeola Olamilekan ya baiyana mana bayan sun kammala zaman a jiya talata.

Olamilekan ya ce ana bukatar karin lokaci don baiwa Gwamnatin Taraiyya damar Kammala wasu aiyuka da ake ci gaba da yi a karkashin Kasafin kudin shekara 2025.

Olamilekan ya ce an yi wannan tsawaitawan ne saboda Najeriya za ta cigaba da gudanar da kasafin kudi guda daya rak daga watan Afrilun badi don inganta amfani da kudaden da aka ware da kuma ba da damar kammala muhimman aiyukan samar da ababen more rayuwa.

A bangaren Majalisar Wakilai kuma Dan Majalisa Daga Jihar Jigawa Abubakar Hassan Fulata yayi bayanin dalilin da ya sa Majalisa ta dauki wannan mataki na tsawaita Kasafin Kudin shekra 2924 da na 2025 din cikin gaggawa Majalisa ta tafi hutun karshen shekara sai ranan 27 ga watan Janairu na shekara 2026 za su dawo bakin aiki.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Jihar Ekiti Ta Aiwatar Da Dokar Haraji
Next Post: Anyi Rashin Mutane Da Yawa Yayinda Bom Ya Fashe Ana Sallar Magariba Maiduguri

Karin Labarai Masu Alaka

Dan Hamayya Ya Amince Da Faduwa A Zaben Kasar Benin Afrika
Kungiyar Kiristoci Ta Karyata Kubutar Da Mambobin Su A Kaduna Afrika
Gobara Ta Lalata Shaguna Da Gidajen Abinci A Gombe Labarai
Hukumar Tsaro Ta DSS Ta Aika Sammaci Dr. Yusuf Baba-Ahmed Labarai
Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Najeriya Ta Tabbatar Da Kyautata Rayuwar Mambobin ta Labarai
Nuhu Ribadu Ya Mika Dalibai 100 da Aka Ceto Ga Gwamnatin Jihar Neja Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Yanayin Yunwa Yana Kara Ta’azarra A Somaliya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kungiyoyin Mata A Jihar Filato Sunyi Gangamin Samun Jagorancin Siyasa Afrika
  • Na Yi Murabus Ne Don Amurka Ta Keta Haddin Iraniyawa Amurka
  • Kocin Zambia Na Mata Ba Lafiya Labarai
  • Jama’ar Kasar Iran Sun Bayyana Goyon Baya Ga Ayatollah Mojtaba Khameni Afrika
  • Turkiyya Ta Zargi Alakar Isra’ila Da Somaliya Afrika
  • Iran Zata Mayarwa Amurka Martanin Harin Kharg Afrika
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Shugaban Makaman Nukiliya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.