Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kungiyar Kwadago Ta Shirya Zanga-Zanga A Najeriya
Published: December 17, 2025 at 5:13 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gabannin zanga-zangar ƙasa baki ɗaya da Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC) za ta gudanar a yau laraba, rundunar ‘yan sanda ta tura jami’an tsaro na musamman domin tabbatar da zaman lafiya da hana tashin hankali.

NLC ta jaddada cewa ba za ta janye zanga-zangar ba, wadda aka shirya sakamakon tabarbarewar tsaro, tsadar rayuwa, da sauran matsalolin ma’aikata.

Kakakin ƙungiyar, Benson Upah, ya yi gargaɗi cewa duk wani yunƙurin kawo cikas ko cutar da ko da mutum ɗaya zai iya haifar da yajin aikin ƙasa baki ɗaya na dindindin.

Ƙungiyar ta ce ta samu bayanan sirri na yiwuwar shigar ‘yan daba ko ‘yan siyasar haya cikin zanga-zangar, tare da kiran mambobinta da al’umma su kasance cikin lumana da haɗin kai.

NLC ta bayyana zanga-zangar a matsayin matakin ‘yan ƙasa gaba ɗaya na neman ingattaccen tsaro da gyaran shugabanci, tana mai kira ga ‘yan sanda su kare ‘yancin jama’a na taruwa don bayyana koke-koken su bisa dokar kasa.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Wani Jirgi Yayi Saukar Angulu Ba Shiri
Next Post: Lawal, Filin Wasa Na Rashidi Yekini Ko Turai Iyaka

Karin Labarai Masu Alaka

Masu Ruwa da Tsaki akan Lamurran Siyasa sun Fara Maida Martani akan Matakin da Ministan Labaran Nigeria da wayar da kan Jama,a Idris Malagi na korar Daya Daga cikin Ma,aikatansa Saboda dalilai na Siyasa. da tsakiayar ranar Wannan larabace dai Mataimakin na Musamman akan yada Labarai ga Minista Malagi Malam Rani,u Ibrahim ya fitar da Wata sanarwar cewa Ministan ya Dakatar da Daya Daga cikin Ma,aikatansa Mai Suna Sa,idu Enagi Saboda ya fitar da Wani bayani a Kafar yada Labarai na sada zumunta dake Nuna Ministan ya shirya tsaf Domin takarar Gwamnan Jihar Neja a 2027. Malam Sa,idu Etsu Tsohon Dantakarar Shugaban cin Jam,iyyar APC a Nigeria Yace Matakin da Ministan ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu lokaci baiyi ba..ceu.. Shima Dattijon Siyasa a Jihar Neja Alh.Awaisu Giwa Kuta Yace Matakin da Ministan Labaran ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu Jihar Neja zaman Makoki Ake na fotinar Yan ta,adda ba wai Batun Neman Mukamin Siyasa ba..ceu .in.. To Sai jigon Jam,iyyar PDP Mai Adawa a Nigeria Hon.Yahaya Ability Yace Akwai kuskure Babba da Ministan ya tabka a dai dai Wannan Zamani na Siyasa duk da cewa Jihar Nejan na cikin Yanayi na masifar Yanbindiga..ceu..in .. Azaben Shekara ta 2023 Malagi ya kara yayi Takara Gwamnan Jihar Neja a jam,iyyar APC inda Gwamna Umar Bago ya kadashi a zaben fidda Gwani. Martanin Wasu ‘Yan Najeriya Ga Ministan Labarai Bisa Korar Dadiminsa Najeriya
Yanbindiga sun Kashe mutun guda tare da yin garkuwa da mutane kimanin 100 a Jihar Nejan Najeriya. Najeriya
Wata Biyu Najeriya Bata Bada Lasisin Shigo Da Mai Daga Ketare Ba Labarai
Jihar Gombe Ta Saka Hannu Kan Yarjejeniya Da Kamfanonin Tunisiya Kimiya
An Bude Makarantu A Najeriya Najeriya
Gwamna Ododo Ya Gargadi Sarakunan Gargajiya Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya
  • Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran
  • MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan
  • Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • An Gudanar Da Addu’o’i Na Musamman Don Neman Zaman Lafiya Labarai
  • Bangladesh Tasamu Rangwamen Harajin Da Amurka Ta Kakaba Mata Labarai
  • Fiye Da Mutane 200 Sun Rasa Rayukansu A Wajen Hakar Ma’adanai Labarai
  • Farashin Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Labarai
  • Kasar Spain Zata Bada Diyya Ga Iyalen Wadanda Da Suka Rasu A Hatsarin Jirgin Kasa Labarai
  • Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Guinea Bissau Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shirin Ga Fili GA Doki Shirye-Shirye
  • Kasar Ukraine Ta Yabawa Tarayyar Turai Bisa Bata Tallafi Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.