Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Kungiyar Kwadago Ta Shirya Zanga-Zanga A Najeriya
Published: December 17, 2025 at 5:13 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gabannin zanga-zangar ƙasa baki ɗaya da Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC) za ta gudanar a yau laraba, rundunar ‘yan sanda ta tura jami’an tsaro na musamman domin tabbatar da zaman lafiya da hana tashin hankali.

NLC ta jaddada cewa ba za ta janye zanga-zangar ba, wadda aka shirya sakamakon tabarbarewar tsaro, tsadar rayuwa, da sauran matsalolin ma’aikata.

Kakakin ƙungiyar, Benson Upah, ya yi gargaɗi cewa duk wani yunƙurin kawo cikas ko cutar da ko da mutum ɗaya zai iya haifar da yajin aikin ƙasa baki ɗaya na dindindin.

Ƙungiyar ta ce ta samu bayanan sirri na yiwuwar shigar ‘yan daba ko ‘yan siyasar haya cikin zanga-zangar, tare da kiran mambobinta da al’umma su kasance cikin lumana da haɗin kai.

NLC ta bayyana zanga-zangar a matsayin matakin ‘yan ƙasa gaba ɗaya na neman ingattaccen tsaro da gyaran shugabanci, tana mai kira ga ‘yan sanda su kare ‘yancin jama’a na taruwa don bayyana koke-koken su bisa dokar kasa.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Wani Jirgi Yayi Saukar Angulu Ba Shiri
Next Post: Lawal, Filin Wasa Na Rashidi Yekini Ko Turai Iyaka

Karin Labarai Masu Alaka

Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
An Bukaci Sabbin Shugabanni Su Yi Jagoranci Nagari da Inganta Ayyukan Jama’a Labarai
Sabuwar Shekarar Musulunci: Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Yi Kira Da A Yawaita Addu’o’i Da Haɗin Kai Afrika
Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Bukaci Musulmi Su Rungumi Tausayi Da Ƙaunar Juna Afrika
Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Tada Kayar Baya Sun Tayar Da Bom A Maiduguri Labarai
  • Gwamnatin Najeriya Tana Saka Ido Akan Matsalolin Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Iran Ta Kama Wasu ‘Yan Leken Asiri Afrika
  • Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine Labarai
  • Gwamnatin Jihar Yobe: Ana Cin Zarafin Fursunoni A Gidan Gyaran Halin Potiskum Tsaro
  • Wani Ya Yiwa ‘Yar Sa Mai Shekaru 8 Fyade A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NLC Ta Yabawa Gwamnan Gombe Inuwa Yahaya Najeriya
  • Shugaba Tinubu Ya Umarci Janye ‘Yan Sanda Masu Gadin Ministoci Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.