Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

“Banga Abun Da Zai Canza Ba A Nadin Janar Christopher Ministan Tsaro”
Published: December 3, 2025 at 3:10 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

“Sulhu da ‘yan bindiga, Boko Haram, da duk wani dan ta’adda shine mafita a Najeriya” Rt. Hon. Aminu Abdulfatah. (Tsohon Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna).

Mun gani ai yake yake da akeyi a duniya, kamar na Ukraine da Rasha, Falasdin da Izra’il duk yanzu sulhu ake kokarin yi domin asamu mafita.

Don haka ya kamata a fadakar da Fulani asaka su a makarantu domin zama mutane masu muhimmanci a cikin al’ummah. Hakkokin su da aka tauye a basu, a yiwa kowane dan kasa adalci.

An yi a baya mun gani, lokacin da masu tada kayar baya a yankin Neja Delta, sulhu akayi dasu a lokacin Shugaban kasa marigayi Umaru Musa ‘Yar-adua.  Aka biya musu bukatun su, aka kaisu makarantu, yanzu ga sunan sun zama manyan mutane, me zai sa baza’a yi ma wadannan ba.

Ya kara da cewar ai tarihi bai manta abu da ya wuce, don kuwa sabon Ministan Janar Christopher Musa, shi ne tsohon hafsan tsaron kasar wanda ya bar mukamin a ‘yan kwanaki, amma matsalar tsaro bata kare ba a kasar lokacin sa. To abun da bai yi a wancan lokacin ba, ya zai iya yin shi a yanzu? Babbar fatar mu dai itace Allah ya bashi ikon yin maganin matsalar, amma dai abu ne mai wuya.

Sau da yawa akan sa siyasa a cikin harkokin tsaro, wanda hakan ba zai haifawa kasar da wani alkhairi ba. Da yawa kuma ana ganin cewar ministan tsaro yana bada umurni ga shugabanin tsaro, ba haka abun yake ba, don kuwa suna da damar ganin shugaban kasa a kowane lokacin.

Shi yasa idan akan ga laifin Badaru to ba’a yi mishi adalci ba. Amma dai koma me ake tunani zamu sa ido don ganin irin rawar da zai taka, wadda bai yi ta ba a lokacin da yake jagoranatar sojojin kasar. Ai sauya suna ko matsayi ba shi ne aiki ba, aiki a zuci ya ke da kuma son kasa, sune abubuwan da zasu taimaka a kawo karshen matsalar.

Akwai bukatar gwamnati ta yi tattaunawa ta massamman da ‘yan ta’addar, aji matsalolin su, a yi sulhu da su, a baiwa kowa hakkin shi don samun zaman lafiya mai dorewa ga al’umar kasa. Kada kuma a manta wasu da yawa suna son a cigaba da wannan yakin don kuwa ta nan suke samun kudi.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: FIFA Na Shirin Fadada Babban Na’urar VAR A Gasar Cin Kofin Duniya 2026.
Next Post: Abba Kabir: Zamu Samar da Jirage Marasa Matuka A Kano

Karin Labarai Masu Alaka

Jami’an Tsaro Na Amfani Da Damar Su Wajen Cin Zarafin Jama’a Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Murkushe Wani Yunkurin Juyin Mulki A Jamhuriyar Benin Afrika
Tinubu Ya Maye Gurbin Badaru Da Tsohon Soja Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kwankwaso Yayi Kakkausar Lafazi Bayan Ficewar Abba Kabir Yusuf Daga NNPP Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Farashin Dalar Amurka Ya Tashi Ranan Juma’a Amurka
Real Madrid: Ta Kori Xabi Alonso Bayan Rashin Nasara A Wasan Kofin Sfaniya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari Da Makami Mai Linzami
  • Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin
  • Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Akwai Bukatar Bin Dokokin Tuki A Kan Hanyoyi Labarai
  • Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine Labarai
  • Jami’ar Tarayya A Gombe Ta Karyata Harin ‘Yan Bindiga Najeriya
  • An Bude Kamfanin Sarrafa Ma’adanai A Kasar Mozambique Labarai
  • Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Lumbala Shekaru 30 Bisa Laifin Cin Zarafi Labarai
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Afrika
  • Tsohon Shugaban Brazil Bolsanaro Zai Tafi Gidan Yari Labarai
  • Hukumar DSS Ta Sake Kama Abubakar Malami Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.