Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

“Banga Abun Da Zai Canza Ba A Nadin Janar Christopher Ministan Tsaro”
Published: December 3, 2025 at 3:10 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

“Sulhu da ‘yan bindiga, Boko Haram, da duk wani dan ta’adda shine mafita a Najeriya” Rt. Hon. Aminu Abdulfatah. (Tsohon Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna).

Mun gani ai yake yake da akeyi a duniya, kamar na Ukraine da Rasha, Falasdin da Izra’il duk yanzu sulhu ake kokarin yi domin asamu mafita.

Don haka ya kamata a fadakar da Fulani asaka su a makarantu domin zama mutane masu muhimmanci a cikin al’ummah. Hakkokin su da aka tauye a basu, a yiwa kowane dan kasa adalci.

An yi a baya mun gani, lokacin da masu tada kayar baya a yankin Neja Delta, sulhu akayi dasu a lokacin Shugaban kasa marigayi Umaru Musa ‘Yar-adua.  Aka biya musu bukatun su, aka kaisu makarantu, yanzu ga sunan sun zama manyan mutane, me zai sa baza’a yi ma wadannan ba.

Ya kara da cewar ai tarihi bai manta abu da ya wuce, don kuwa sabon Ministan Janar Christopher Musa, shi ne tsohon hafsan tsaron kasar wanda ya bar mukamin a ‘yan kwanaki, amma matsalar tsaro bata kare ba a kasar lokacin sa. To abun da bai yi a wancan lokacin ba, ya zai iya yin shi a yanzu? Babbar fatar mu dai itace Allah ya bashi ikon yin maganin matsalar, amma dai abu ne mai wuya.

Sau da yawa akan sa siyasa a cikin harkokin tsaro, wanda hakan ba zai haifawa kasar da wani alkhairi ba. Da yawa kuma ana ganin cewar ministan tsaro yana bada umurni ga shugabanin tsaro, ba haka abun yake ba, don kuwa suna da damar ganin shugaban kasa a kowane lokacin.

Shi yasa idan akan ga laifin Badaru to ba’a yi mishi adalci ba. Amma dai koma me ake tunani zamu sa ido don ganin irin rawar da zai taka, wadda bai yi ta ba a lokacin da yake jagoranatar sojojin kasar. Ai sauya suna ko matsayi ba shi ne aiki ba, aiki a zuci ya ke da kuma son kasa, sune abubuwan da zasu taimaka a kawo karshen matsalar.

Akwai bukatar gwamnati ta yi tattaunawa ta massamman da ‘yan ta’addar, aji matsalolin su, a yi sulhu da su, a baiwa kowa hakkin shi don samun zaman lafiya mai dorewa ga al’umar kasa. Kada kuma a manta wasu da yawa suna son a cigaba da wannan yakin don kuwa ta nan suke samun kudi.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: FIFA Na Shirin Fadada Babban Na’urar VAR A Gasar Cin Kofin Duniya 2026.
Next Post: Abba Kabir: Zamu Samar da Jirage Marasa Matuka A Kano

Karin Labarai Masu Alaka

Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
Gwamnonin Arewa “Mun Amince Da Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Barau Jibril: Mu Ba ‘Yan Amshin Shata Bane A Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Najeriya Da Amurka Sun Amince Su Haɗa Kai Don Inganta ’Yancin Addini Da ƙarfafa Tsaro A Nijeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Christ Musa Ministan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Rasha Takai Hari Ukraine Da Jirgi Marar Matuki Afrika
  • Kasar Ghana Ta Tono Gold Na Miliyoyin Kudade Kimiya
  • Sojoji Sun Dakile Harin ’Yan Ta’adda a Kukareta Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Turawa Majalisa Sunayen Mutane Biyun Da Zasu Shugabanci Sashin Albarkatun Mai Labarai
  • Rikici Tsakanin NNPC Da Kungiyar Gwamnoni Akan Gibin Kudade Labarai
  • Za’a Ninka Shekarun Zama A Gidan Kurkuku Ga Masu Auren Jinsi A Senegal Afrika
  • Kimanin Mutane 200 Ne Suka A Mutu A Wani Harin Jirgin Yakin Sojin Najeriya Afrika
  • Kotun Amurka Tana Tuhumar Wani Dan Jarida Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.