Iran ta bada tabbacin ci gaba da yaki tare da rufe mashigin Hormuz a matsayin abin da za ta iya kaiwa ga Amurka da Isra’ila, in ji sabon Jagoran juyin juya halin Musulunci Mojtaba Khamenei a ranar Alhamis a cikin kalaman farko da aka danganta shi da shi tun bayan da ya gaji mahaifinsa da aka kashe.
Khamenei bai bayyana da kansa ba kuma wani mai gabatarwa na gidan talabijin na kasar ne ya karanta jawabin. Ba a fitar da wani hotonsa ba tun bayan harin da Isra’ila ta kai a farkon yakin da ya yi sanadiyar mutuwar yawancin iyalansa, ciki har da mahaifinsa da matarsa.
Sanarwar ta jiya Alhamis ta dau hankali, inda Khamenei ya yi kira ga kasashen da ke makwabtaka da Iran da su rufe sansanonin Amurka da ke yankinsu tare da gargadin cewa Iran za ta ci gaba da kai musu hari.
“Ina tabbatar wa kowa da kowa cewa ba za mu yi sakaci da daukar fansar jinin shahidan ku ba,” in ji malamin nan mai tsaurin ra’ayi wanda ke da kusanci da babbar rundunar sojan Iran.
Khamenei ya kara da cewa, “Bukatar da jama’a ke da, ita ce mu ci gaba da samar da ingantaccen tsaro da kuma sanya makiya su yi nadama. Dole ne a ci gaba da yin amfani da shingen toshe mashigin ruwa na Hormuz,” Khamenei ya kara da cewa, yayin da yake magana kan hanyar jigilar kayayyaki da kashi biyar na man duniya ke bi ta gabar tekun Iran.


