Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno
Published: December 18, 2025 at 9:00 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mayakan Boko Haram sun sace sabon mataimakin shugaban karamar hukuma da kansiloli a jihar Borno dake arewacin Najeriya

Wasu da ake zargin mambobin kungiyar Boko Haram ne sun sace sabon Mataimakin Shugaban Karamar Hukumar Biu da wasu kansiloli biyu, a kan hanyar Kamuya Buni Yadi, a Jihar Borno.

Majiyoyi da ke kusa da iyalansu sun bayyana sunan Mataimakin Shugaban a matsayin Alhaji Saidu. Kansilolin biyu masu wakiltar mazabun Zarawuyaku da Miringa.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa an zaɓi wadanda aka sace ne kwanaki biyar da suka gabata, a zaben kananan hukumomi da aka gudanar ranar Asabar da ta wuce.

Daya daga cikin majiyoyin ya bayyana cewa lamarin ya faru ne da yammacin ranar Laraba, kuma ya shafi wasu matafiya da ke cikin wata motar Hizbah Hummer.

“Gaskiya ne, Alhaji Saidu da kansilolin biyu an sace su ne da hannun wadanda ake zargin ‘yan Boko Haram/ISWAP ne, a tsakanin kauyen Kamuya da hanyar Buni Yadi.

“An sace su tare da wasu fasinjoji da ba a tantance su ba, wadanda ke tafiya cikin wata motar Hizbah daga garin Potiskum na Jihar Yobe zuwa Biu.

“Daya daga cikin kansilolin da aka sace shi ne tsohon Mataimakin Shugaban Karamar Hukumar Biu na nan kusa kuma muna rokon gwamnati da hukumomin tsaro su kara kaimi wajen ceto su da sauran wadanda aka kama” in ji shi.

Kokarin jin ta bakin kakakin rundunar ‘yan sanda ta Jihar Borno, ASP Nahum Kenneth Daso, bai yi nasara ba, domin ba a samu damar tuntubarsa ta waya ba, haka kuma bai amsa sakonnin da aka aike masa ba.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: A Kowacce Rana Kasar China Tana Sayan Danyen Mai Ganga Dubu 600 Daga Kasar Venezuela
Next Post: Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati

Karin Labarai Masu Alaka

An Kaiwa Sojojin Ghana Hari A Lebanon Afrika
Ana Zargin Wani Dan Kasar Libya Da Fataucin Mutane Tsaro
Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yaki Da Akeyi Tsakanin Isra’ila Da Amurka Afrika
Hare Hare A Kasar Congo Ya Jikkata Mutane Da Dama Afrika
Zanga-Zangar Adawa Da Harin Amurka Da Isra’ila Ya Zamo Tarzoma A Pakistani Afrika
Amurka Da Tarayyar Turai Sun Fidda Sanarwa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi
  • Shugaban Amurka Yayi Watsi Da Tattaunawar Kawo Karshen Yaki Da Iran
  • Iran Zata Mayarwa Amurka Martanin Harin Kharg
  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Najeriya Ta Kai Wasan Kusa Da Na Karshe A Wasan Dambe Na Matasan Afirka Wasanni
  • Shugaba Trump Ya Janye Karbar Kudin Fito Daga Wasu Kasashen Turai Amurka
  • Anfara Tantance Lafiyar Maniyyatan Jihar Gombe Kiwon Lafiya
  • Zaman Lafiya Yafara Dawowa A Sudan Afrika
  • Yau Shekaru 60 Da Kisan Gilla Ga Sir. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tsohuwar Ministan Albarkatun Mai Ta Bayyana A Kotu Najeriya
  • Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Roger Lumbala Shekaru 30 Labarai
  • Yan Najeriya na ci gaba da maida martani akan sabuwar dokar zabe da majalisar Dattawan kasar ta Amince dashi Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.