Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati
Published: December 18, 2025 at 10:56 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 19, 2025

Gwamnatin Tarayya ta ɗauki matakai don farfaɗo da Maɗaba’ar Gwamnati da aka yi watsi da ita, bayan shekaru ana tafka asara.

Gwamnatin Tarayyar Najeriya za ta ɗauki tsauraran matakai domin kawo ƙarshen shekaru na asara da sakaci bayan Ministan yaɗa labarai da wayar da kan al’umah, Alhaji Mohammed Idris, ya kai ziyarar duba Maɗaba’ar Gwamnati da aka daɗe da yin watsi da ita a Abuja, a ranar Alhamis.

A yayin ziyarar, Ministan ya bayyana matuƙar damuwa game da halin da wurin yake ciki.

Ya bayyana cewa watsi da kamfanin ya jawo asarar biliyoyin naira, wanda abu ne da ba za a amince da shi ba, kuma ya saɓa wa salon Gwamnatin Tarayya da ta tanada, ɗaukar mataki da kuma amfani da dukiyoyin jama’a yadda ya dace, a ƙarƙashin Manufar “Renewed Hope” ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Ministan ya tuna cewa an aza tubalin ginin cibiyar tun a shekarar 2001 a zamanin tsohon Shugaba Olusegun Obasanjo, inda ya bayyana cewa aikin ya kai kusan kashi 70 cikin 100 na kammalawa, tare da samar da manyan na’urorin ɗab’i tun a shekarar 2007. Abin mamaki kuma, yawancin injinan da aka shigo da su daga ƙasashe irin su Jamus da Indiya har yanzu ba a buɗe su daga akwatunan su na asali ba fiye da shekara goma, inda wasu daga cikin fasahohin su ma suka zama tsofaffi sakamakon dogon sakaci.

Ya ce: “Abu ne mai taɓa zuciya ganin irin wannan asara a tsakiyar Abuja,” inji Ministan, yana mai cewa, “A daidai lokacin da gwamnati take ƙoƙarin tanadin albarkatu da dogaro da kai, abin ba zai yiwu ba a bar irin wannan babban jari ya lalace shekara da shekaru.”

Maɗaba’ar Gwamnati, wadda ke aikin bugun takardun Gwamnatin Tarayya, ita ce ke da alhakin gurza muhimman takardun ƙasa, ciki har da Jaridar Gwamnatin Tarayya (Federal Government Gazette) da sauran muhimman wallafe-wallafen Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai.

Ministan ya ce tsawon lokacin da maɗaba’ar ta tsaya ba tare da aiki ba ya tilasta gwamnati ta riƙa fitar da ayyukan ɗab’i zuwa waje, alhali ya kamata a yi su a cikin gida, lamarin da ke rage inganci da ƙarfin ƙasa.

Binciken ya kuma nuna cewa muhimman kayayyakin more rayuwa a wurin, ciki har da sabon janareta mai ƙarfin 2000 KVA da aka girka tun a shekarar 2011, bai taɓa aiki ba, wanda ke nuna yadda aka bar dukiyoyin jama’a ba a amfani da su.

Ministan ya samu rakiyar Babban Sakatare na Dindindin, Daraktan Riƙo da ke kula da sashen, da sauran manyan jami’an ma’aikatar.

Ministan ya bayyana cewa sun yi ziyarar ne domin shugabanni su ga halin da ake ciki da idon su, su yi cikakken nazari, sannan su yanke sahihan shawarwarin gudanarwa.

Ya ce: “Mun zo ne domin mu gani da idon mu. za mu koma mu gabatar da shawarwari masu ma’ana ga ga Shugaban Ƙasa da majalisar zartarwa ta tarayya kan mafi kyawun hanyoyin farfaɗo da wannan Maɗaba’ar Gwamnati tare da amfani da ita domin amfanin ‘yan Nijeriya.”

Ministan ya jaddada cewa Gwamnatin Tarayya ba za ta ci gaba da yin shiru kan lalacewar dukiyoyin ƙasa ba, inda ya tabbatar da cewa za a ɗauki matakai masu ƙarfi domin dawo da darajar jarin da aka riga aka zuba da kuma hana ƙarin asara.

Ya kuma sake jaddada ƙudirin ma’aikatar yaɗa labarai da wayar da kai na gaskiya, kyakkyawan shugabanci da ingantaccen sarrafa albarkatun jama’a, bisa ga umurnin Shugaba Tinubu na cewa duk nairar da aka kashe dole ne ta haifar da wani amfani ga ‘yan Najeriya.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno
Next Post: Fintiri: Zamu Maida Jihar Adamawa Sabuwar Duniya

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji A Kauyen Wanka Jihar Filato Afrika
An Kashe Mutane 169 A Wani Harin Sudan Ta Kudu Afrika
Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya Afrika
Hukumar Tsaron Teku A Libya Tafara Janye Jirgi Mai Dauke Da Iskar Gas Labarai
Shugabar Kungiyar Cinikayya Ta Duniya Ta Bukaci Kasashe Su Gyara Harkokin Cinikayya Afrika
Haryanzu Abubakar Malami Da Dansa Suna Hannun Hukumar EFCC Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Da Arzikin Mu: Bamu Ba Bautawa Turawan Yamma Afrika
  • Iran Tabada Tabbacin Cigaba Da Rufe Mashigar Hormuz Afrika
  • Isra’ila Ta Dau Alwashin Kawo Karshen Falasdi Labarai
  • Sojin Kasar Congo Da ‘Yan Tawaye Sun Kara Shiga Yankin Uvira Labarai
  • Kasar Uganda Ta Tsare ‘Yan Jam’iyyun Adawa Dubu Biyu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Samu Nasarar Karbo Karin Yara 130 Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Zata Karbi ‘Yan Gudun Hijirar Da Amurka Ta kora Afrika
  • Sakataren Gwamnatin Amurka Ya Bayyana Bawa Kungiyoyin Agaji Damar Kai Taimako Sudan Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.