An shiga jimami a masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood bayan rasuwar tsohuwar jarumar fina-finai, Wasika Ismail.
Rahotanni sun tabbatar da cewa marigayiyar ta rasu bayan fama da rashin lafiya, lamarin da ya jawo alhini da ɗimuwa tsakanin ‘yan uwa, abokan aiki da masoyanta a faɗin ƙasar nan.
Marigayiya Wasika Ismail ta kasance ɗaya daga cikin fitattun tsoffin jaruman Kannywood da suka taka rawa wajen bunƙasa masana’antar fina-finan Hausa tun a shekarun baya. Ta shahara wajen fitowa a fina-finai masu ɗauke da darussa da al’adun Hausawa, inda ta samu karɓuwa a zukatan masu kallo saboda ƙwarewarta da salon gudanar da rawa.
Mutane da dama daga cikin ‘yan masana’antar Kannywood sun bayyana alhininsu kan rasuwar tata, suna masu bayyana ta a matsayin mace mai mutunci, biyayya da son taimakon jama’a.
Wasu daga cikin abokan aikinta sun bayyana cewa rasuwarta babban gibi ne ga masana’antar, musamman ganin yadda ta bayar da gudunmawa wajen haɓaka harkar fina-finan Hausa da kuma tarbiyyar matasa ta hanyar shirye-shiryen da take fitowa a ciki.
Masoya da mabiyanta sun ci gaba da bayyana alhini a shafukan sada zumunta, inda suke addu’ar Allah Ya jikanta da rahama, Ya gafarta mata kura-kuranta tare da ba iyalanta da ‘yan uwanta haƙurin jure wannan babban rashi.
An gudanar da jana’izarta bisa koyarwar addinin Musulunci tare da halartar ‘yan uwa, abokai da wasu daga cikin fitattun jaruman Kannywood.


