Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Gombe Ta Yi Kira Ga Jami’o’i Su Tallafa Wa Gwamnati Ta Hanyar Bincike Da Ƙirƙire-ƙirƙire
Published: July 7, 2026 at 5:02 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Gombe ta yi kira ga jami’o’i da sauran manyan makarantun gaba da sakandare da su ƙara taka rawar gani wajen magance matsalolin al’ummomin da suke ciki tare da tallafa wa gwamnati ta hanyar bincike da kirkire-kirkire.

Mataimakin Gwamnan jihar Gombe, Manassah Daniel Jatau, ne ya bayyana hakan yayin da ya karɓi tawagar shugabannin Jewel University ƙarƙashin jagorancin Mataimakin Shugaban Jami’ar, Yahya Ibrahim Yero, a ziyarar girmamawa da suka kai masa.

Dr. Jatau ya ce ya kamata jami’o’i su gina haɗin gwiwa na dabaru domin samun ɗorewar kuɗaɗen gudanarwa, su tabbatar da ingancin ilimi, sannan su yi amfani da kafafen yaɗa labarai wajen bayyana shirye-shiryensu da nasarorin da suke samu. Ya ƙara da cewa babu wata jami’a da za ta bunƙasa idan ta ware kanta daga al’ummar da take ciki.

Ya kuma bayyana cewa jihar Gombe yanzu tana da jami’o’i biyar, lamarin da ya ce babban ci gaba ne a fannin ilimi. Haka kuma ya buƙaci jami’ar ta haɗa kai da gwamnatin jihar wajen fuskantar matsalolin tsaro.

Mataimakin gwamnan ya kuma bayyana cewa ana shirin gudanar da bukukuwan cika shekaru 30 da ƙirƙirar Jihar Gombe, inda ya gayyaci jami’ar da ta ba da gudummawa ta hanyar bincike da shawarwarin masana domin tabbatar da nasarar bikin.

Dr. Jatau ya tabbatar wa jami’ar da ci gaba da samun goyon bayan gwamnatin jihar, tare da ƙarfafa gwiwar shugabanninta su ci gaba da tuntuɓar gwamnati idan akwai buƙatar taimako a hukumance.

Tun da farko, Mataimakin Shugaban Jewel University, Farfesa Yahya Ibrahim Yero, ya ce manufar ziyarar ita ce ƙarfafa haɗin gwiwa da gwamnatin jihar.

Ya bayyana cewa jami’ar na gudanar da shirye-shiryen karatu guda 25 da National Universities Commission ta amince da su.

Haka kuma ya bayyana cewa wanda ya kafa jami’ar ya samar da guraben karatu ga ɗalibai marasa galihu, musamman ‘yan asalin Jihar Gombe da sauran ɗaliban yankin Arewa maso Gabas.

Farfesa Yero ya sake jaddada kudirin jami’ar na samar da waɗanda suka kammala karatu masu ilimi, ƙwarewa da kyawawan ɗabi’u domin ba da gudummawa ga ci gaban ƙasa.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Sabuwar Dama Ga Masu Zaɓe: INEC Ta Tsawaita CVR Zuwa Ƙarshen Yuli
Next Post: Sarakunan Gombe Da Zazzau Sun Yi Kira Ga ‘Yan Najeriya Su Rungumi Haɗin Kai Da Zaman Lafiya

Karin Labarai Masu Alaka

Dakaru Sun Hallaka ’Yan Ta’adda Masu Yawa – DHQ Afrika
Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin Afrika
Kamfanin Jiragen Saman Ethiopia Zai Kafa Babban Filin Jirgi Afrika
Fafaroma Leo Zai Ziyarci Kasashen Afirka Amurka
Matatar Man Dangote Ta Samu Tagomashi Daga Abokan Hulda Najeriya
Gwamnan Neja Bago Na Cin Zarafin Talakawan Da Suka Zabe Shi Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • AFCON 2025, Jerin Abubuwan Da Aka Haramta Wa Magoya Baya Wasanni
  • Magajin Garin Istanbul Dake Kurkuku Ya Bukaci A Gudanar Da Zabe Labarai
  • Kasashen Daular Larabawa Tare Da Saudiya Da Jordan Sunyi Allah Wadai Da kasar Israel Afrika
  • Wani Bincike Ya Nuna Cewar Da Wuya Iran Ta Bude Mashigin Hormuz Afrika
  • Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya Najeriya
  • An Ga Watan Ramadan A Najeriya Da Nijar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Tayi Barazanar Rage Tallafinta Wa Sudan Ta Kudu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.