Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Hukumar EFCC Ta Kwace Gidan Tsohon Antoni Janar Abubakar Malami
Published: December 17, 2025 at 9:53 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Kasa (EFCC) ta rufe wani gida da ke da alaka da tsohon Antoni Janar na ƙasa kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, SAN, a daren Laraba, a matsayin wani bangare na binciken cin hanci da rashawa da ake yi masa.

Rahotanni sun ce jami’an EFCC tare da jami’an tsaro sun isa gidan, inda aka ce Nana Hadiza Buhari, ’yar tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari kuma matar Malami, tana nan a lokacin da aka gudanar da aikin.

Matakin na zuwa ne yayin da EFCC ke ci gaba da tsare Malami bisa zargin cin hanci da rashawa, halasta kudaden haram da wasu laifuka da suka shafi kudaden Abacha da aka kwato.

EFCC ta bayyana cewa belin da aka ba Malami a baya an soke shi saboda rashin cika sharudda, kuma har yanzu yana hannun hukuma domin ci gaba da bincike.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, babu wata sanarwa daga bangaren Malami ko iyalan Buhari kan lamarin.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai
Next Post: ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba

Karin Labarai Masu Alaka

ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
Kungiyar Mata Manoma A Najeriya Ta Raba Kyautar Abinci A Gombe Afrika
Pantami Ya Bayyana Dalilin Mayar Da Zaben Sa Abuja Afrika
Masarautar Borgu a Jihar Neja na neman daukin Gwamnatin Najeriya akan matsalar rashin tsaro Najeriya
Gwamnatin Najeriya Ta Tallafa Wa ’Yan Sanda Da Motoci Afrika
Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Prime Ministan Senegal Ya Bayyana Shirin Sauya Sheka Afrika
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Gabatar Da Kudi Fiye Da Naira Triliyan 58 A Matsayin Kasafin 2026 Najeriya
  • Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce! Najeriya
  • An Murkushe Wani Yunkurin Juyin Mulki A Jamhuriyar Benin Afrika
  • Najeriya, Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Sama Da 80, Sun Ceto 34 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Tayi Baje Kolin Nasarorin Tinubu Afrika
  • IBB: Ba Shakka Abiola Ya Lashe Zaben Yuni 12 Rediyo
  • Ruwan Sama Ya Dai-Daita ‘Yan Gudun Hijira A Gaza Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.