Kotun Tarayya ta hana INEC amincewa da tarukan jam’iyyar ADC da kwamitin Mark ya shirya
Wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja a Najeriya ta umarci Hukumar Zabe ta (INEC) a kasar da kada ta amince ko ta shiga cikin duk wani taron zaɓen shugabannin jihohi (state congresses) da kwamitocin da shugabancin rikon ƙwarya na African Democratic Congress (ADC) suka shirya.
Da take yanke hukunci a ranar Laraba, Mai Shari’a Joyce Abdulmalik ta bayyana cewa alhakin gudanar da irin waɗannan taruka na jihohi yana hannun kwamitocin zartarwa na jihohi na jam’iyyar, ba shugabancin ƙasa ba.
Kotun ta kuma tabbatar da cewa wa’adin shekaru huɗu na kwamitocin aiki na jihohi da kwamitocin zartarwa na jihohi na jam’iyyar ADC na nan daram, kuma suna ci gaba da aiki har sai an gudanar da sahihan taruka bisa ƙa’ida tare da kiran babban taron ƙasa.
Haka kuma, Mai Shari’a Abdulmalik ta ce babu wani tanadi a cikin Kundin Tsarin Mulkin Najeriya ko na jam’iyyar da ke bai wa kwamitin rikon ƙwarya na ƙasa, ƙarƙashin jagorancin David Mark, ikon naɗa kwamitocin da za su gudanar da tarukan jihohi.
Hukuncin ya biyo bayan ƙarar mai lamba FHC/ABJ/CS/581/2026 da wasu masu ƙara suka shigar, suna ƙara a madadinsu da kuma a madadin dukkan shugabannin jihohi da kwamitocin zartarwa na jihohi na jam’iyyar ADC.


