Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Guterres: Babban Kuskure Ne Yadda Isra’ila Ta Kai Farmaki A Gaza
Published: December 3, 2025 at 8:10 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 3, 2025

Babban sakataren MDD, Antonio Guterres, yace akwai babban kuskure kan yadda Isra’ila ta gudanar da farmakin soja a zirin Gaza, kuma akwai kwakkwarar shaidar cewa ta aikata laifuffukan yaki a lokacin hare-haren.

Da yake magana yau laraba a wajen wani taron da kamfanin dillancin labarai na Reuters ke shiryawa, Mr. Guterres yace an yi biris baki daya da illar hare-haren a kan fararen hula da kuma lalata muhallansu a fadin Gaza.

Yace Isra’ila ta ce manufarta ita ce ta murkushe Hamas, amma kuma, ba Hamas din aka murkushe ba.

An kashe mutane fiye da dubu 70 a Gaza a lokacin wannan farmaki na Isra’ila, wanda ya biyo bayan harin da Hamas ta kai ta kashe mutane 1200 tare da kama mutane 251 a watan Oktobar 2023.

Da aka tambaye shi ko akwai alamun an aikata laifuffukan yaki a wannan farmaki na Isra’ila, babban sakataren na MDD yace akwai kwararan dalilai na yarda da cewa an aikata hakan.

An kulla yarjejeniyar tsagaita wuta a yankin tun 10 ga watan Oktoba, amma Isra’ila ta ci gaba da kai hare-hare tare da rushe gine-ginen da take ikirarin cewa cibiyoyin Hamas ne.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Jami’an Tsaro Na Amfani Da Damar Su Wajen Cin Zarafin Jama’a
Next Post: RSF Ta Kasar Sudan, Tana Yin Garkuwa Da Mazauna A Yankin Darfur

Karin Labarai Masu Alaka

Amurka Zata Saidawa Saudiyya Da Jirgin Yaki Samfurin F35 Labarai
Afirka Ta Kudu Ta Bukaci Jakadan Israela Ya Fice Daga Kasar Afrika
Anyi Rashin ‘Yan Jarida 6 A Jihar Gombe Sakamakon Hatsarin Mota Labarai
‘Yan Tawayen Houthi Sunkai Hari Isra’ila Afrika
Shugaba Tinubu Yasa Hannu Kan Dokar Kasafin 2026 Afrika
Farashin Mai Ya Cigaba Da Tashi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kamfanin Bitcoin A Korea Ta Kudu Yayi Kuskuren Turawa Masu Mu’amala Da Kamfanin Kudade Afrika
  • Najeriya Ta Kai Wasan Kusa Da Na Karshe A Wasan Dambe Na Matasan Afirka Wasanni
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi Afrika
  • Hotunan Hawan Sallah A Masarautar Bauchi Afrika
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki Labarai
  • Kasar India Ta Sayi Iskar Gas Daga Iran Labarai
  • Fitaccen Dan Jarida a Sokoto Surajo Dalhatu Sifawa Ya Rasu Najeriya
  • Najeriya Na ƙoƙarin Shiga Gasar Cin Kofin Duniya 2026 Ta Barauniyar Hanya Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.