Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Jami’an Tsaro Na Amfani Da Damar Su Wajen Cin Zarafin Jama’a
Published: December 3, 2025 at 5:57 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Shugabannin Fulani a Jihar Nejan Nigeria sun koka akan yadda suka ce Jami’an Tsaron ‘Yan-banga na cin zarafin Fulanin ba tare da tantance mai laifi ko mara laifi.

Wannan dai yana zuwa ne bayan da aka yi zargin wasu ‘yan bindiga a yankin karamar Hukumar Mashegu sun ci zarafin shugaban kungiyar makiyaya ta Miyatti Allah tare da wasu Fulanin su 13.
Bayanai dai sun nuna cewa ‘yan bangan sun yima wadan nan Fulani daurin goro tare da gana musu azaba da a yanzu haka suna karbar magani a babbar Asibitin Gwamnati dake Kontagora,
Alh. Muhammadu Mabbe, shine shugaban Fulanin na karamar Hukumar Magama da ya shiga hannun wadan nan ‘Yan banga da a yanzu haka yake kwance cikin wani mawuyancin hali, yace ‘yan bangar sun sameshi a kofar gidan Sarkin koso ne a dai dai lokacin da suke kokarin jana’izar wani yaron su da aka kashe.
Shugaban Babban Jami’i a Ma’aikatar Kula da Harkokin Makiyaya ta Jihar Neja Malam Ababakar Kamfanin Bobi yayi karin haske akan irin azabar da aka basu.
Sarkin Fulanin Minna Alhaji Hasan Shiroro, wanda shima a kwanakin baya yace ‘yan bangar sun bindige yaro kuma nan take ya mutu har lahira.
Mun tuntubi shugaban ‘yan bangar na Jihar Neja Nasiru Muhwmmad Manta, yace basu da hannu a ciki, amma kuma zasu gudanar da bincike akan lamarin.
Tini dai masu kare hakkin dan adam suka bayyana damuwa akan wannan lamari Kwamrade Kabiru Idris Jami’i ne a hukumar kare hakkin dan adam ne a Jihar Nejan, inda yace basu yadda da wannan cin zarafin ba.
Suma masana a fannin tsaron da zamantakewa suka nuna bukatar dakatar da irin wannan daukar doka a hannu, don shawo kan matsalolin tsaro da Najeriya ke fama dashi.
Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Tarayya Ta Ce Babu Musguna Wa ’Yan Jarida A Mulkin Tinubu
Next Post: Guterres: Babban Kuskure Ne Yadda Isra’ila Ta Kai Farmaki A Gaza

Karin Labarai Masu Alaka

An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi Afrika
Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Ya Rasu A Abuja Bayan Doguwar Jinya Afrika
Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina Afrika
  • Farashin Mai Yayi Tashin Gwaron Zabi Afrika
  • Iran Ta Kama Wani Jirgin Ruwa Shake Da Mai Labarai
  • Shugaban Amurka Yace Zasu Kakabawa Mashigar Hormuz Takunkumi Afrika
  • Ma’aikatan Tattara Kudin Haraji Sunyi Rikici Da Masu Babura A Bauchi Najeriya
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Wajen Hakar Ma’adanai Dake Jihar Filato Najeriya
  • Kotu A Kasar Tunisiya Ta Daure Wani Babban Dan Kasuwa Da Wasu ‘Yan Majalisa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.