Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Jami’an Tsaro Na Amfani Da Damar Su Wajen Cin Zarafin Jama’a
Published: December 3, 2025 at 5:57 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Shugabannin Fulani a Jihar Nejan Nigeria sun koka akan yadda suka ce Jami’an Tsaron ‘Yan-banga na cin zarafin Fulanin ba tare da tantance mai laifi ko mara laifi.

Wannan dai yana zuwa ne bayan da aka yi zargin wasu ‘yan bindiga a yankin karamar Hukumar Mashegu sun ci zarafin shugaban kungiyar makiyaya ta Miyatti Allah tare da wasu Fulanin su 13.
Bayanai dai sun nuna cewa ‘yan bangan sun yima wadan nan Fulani daurin goro tare da gana musu azaba da a yanzu haka suna karbar magani a babbar Asibitin Gwamnati dake Kontagora,
Alh. Muhammadu Mabbe, shine shugaban Fulanin na karamar Hukumar Magama da ya shiga hannun wadan nan ‘Yan banga da a yanzu haka yake kwance cikin wani mawuyancin hali, yace ‘yan bangar sun sameshi a kofar gidan Sarkin koso ne a dai dai lokacin da suke kokarin jana’izar wani yaron su da aka kashe.
Shugaban Babban Jami’i a Ma’aikatar Kula da Harkokin Makiyaya ta Jihar Neja Malam Ababakar Kamfanin Bobi yayi karin haske akan irin azabar da aka basu.
Sarkin Fulanin Minna Alhaji Hasan Shiroro, wanda shima a kwanakin baya yace ‘yan bangar sun bindige yaro kuma nan take ya mutu har lahira.
Mun tuntubi shugaban ‘yan bangar na Jihar Neja Nasiru Muhwmmad Manta, yace basu da hannu a ciki, amma kuma zasu gudanar da bincike akan lamarin.
Tini dai masu kare hakkin dan adam suka bayyana damuwa akan wannan lamari Kwamrade Kabiru Idris Jami’i ne a hukumar kare hakkin dan adam ne a Jihar Nejan, inda yace basu yadda da wannan cin zarafin ba.
Suma masana a fannin tsaron da zamantakewa suka nuna bukatar dakatar da irin wannan daukar doka a hannu, don shawo kan matsalolin tsaro da Najeriya ke fama dashi.
Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Tarayya Ta Ce Babu Musguna Wa ’Yan Jarida A Mulkin Tinubu
Next Post: Guterres: Babban Kuskure Ne Yadda Isra’ila Ta Kai Farmaki A Gaza

Karin Labarai Masu Alaka

Hamma Saleh Ya Yi Fatali da Bai Wa Pantami Takarar Gwamna a PDP Afrika
Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
NAHCON Ta Fara Shirye-shiryen Dawowar Alhazai Afrika
Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Christ Musa Ministan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
UPF Ta Bukaci Haɗin Gwiwa Da NERDC Domin Gina Al’umma Mai Zaman Lafiya Afrika
Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ambaliyar Ruwa Ya Tilastawa Dubban Jama’a Rasa Muhallensu A Morocco Afrika
  • Hare Hare A Kasar Congo Ya Jikkata Mutane Da Dama Afrika
  • Ukraine Tana Cigaba Da Tattaunawa Da Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Kasar Amurka
  • Kungiyar HPV A Jihar Gombe Ta Jagoranci Yaki Da Karuwar Cutar Daji Afrika
  • ‘Yan Sanda A Tsibirin Bahamas Sun kama Mijin Wata Ba Amurkiya Amurka
  • Shugaban Hukumar NAHCON Ya Yabawa ‘Yan Jarida Kiwon Lafiya
  • Amurka Tana Cigaba Da Kare Jami’in Da Ya Kashe Ba Amurke Amurka
  • Onana Ba Ya Cikin Tawagar Kamaru (AFCON) Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.