Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Gwamnatin Gombe: Babu Hannun mu a Cin Zarafin Kansilan Mazabar Shamaki
Published: December 20, 2025 at 9:45 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Gombe ta musanta zargin da ƙungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International ta yi cewa, ana cin zarafi ko wulaƙanta waɗanda suka soki gwamnatin jahar.

Wata sanarwar da kakakin gwamnatin jahar Ismaila Uba Misilli ya fitar da yammacin Juma’a, ta ce babu ƙamshin gaskiya a zargin da ƙungiyar ta yi bayan wani faifan bidiyo ya nuna ɗaya daga cikin hadiman gwamnan jihar yana marin Kansilar gundumar Shamaki.

A sanarwar, Misilli ya ce bai kamata a riƙa alaƙanta lamarin da gwamnatin jihar ba, har ma ya yi gargaɗi game da saka siyasa kuma ya nesanta hannun wani jami’in gwamnati ko gwamnatin jhar a ciki.

Sanarwar ta ce babu wanda ya fi ƙarfin doka, kuma tuni aka fara ɗaukar matakan bincike dan ɗaukar mataki kan lamarin da ya sha suka daga al’umma.

Sanarwar ta kuma yi gargadin cewa a guji alaƙanta lamarin da gwamna ko gwamnatin jihar, tana mai cewa Gwamna Inuwa Yahaya baya goyon saɓa doka ko cin mutuncin wani.

A yanzu dai ƙungiyoyin da al’umma na jiran ganin matakin da gwamnatin za ta ɗauka a kan wanda ake zargin.

Siyasa

Post navigation

Previous Post: Matatar Man Dangote Ta Samu Tagomashi Daga Abokan Hulda
Next Post: Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi

Karin Labarai Masu Alaka

Kotu A Kasar Tunisiya Ta Daure Wani Babban Dan Kasuwa Da Wasu ‘Yan Majalisa Afrika
Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
Jagoran Kwankwasiya A Najeriya Ya Koma Jam’iyar ADC Labarai
Kotun Tarayya Tabada Belin Nasiru El Rufai Afrika
Gwamnan Jihar Kano Ya Fice Daga Jam’iyar NNPP Siyasa
Akwai Bukatar APC Tayi Gyare-Gyare Kafun Zabe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasashe Biyar Zasu Tura Sojoji Domin Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya A Gaza Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Adamu: “Yakar Cin Hanci Daga Tushe Itace Mafita Daya Tilo” Labarai
  • Kasar Malawi Ta Kaddamar Da Rigakafin Shan Inna Kiwon Lafiya
  • An Gudanar Da Addu’oi Ga Mutane 16 Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe a Australiya Tsaro
  • Amurka Zatayi Amfani Da Sansanonin Birtaniya Amurka
  • Rundunar Operation Endurance Peace Ta Gano Wajen Kera Makamai A Jihar Filato Afrika
  • Kananan Hukumomi Na Kokarin Karbar Kudadensu Daga Jihohi Najeriya
  • Za’a Ninka Shekarun Zama A Gidan Kurkuku Ga Masu Auren Jinsi A Senegal Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.