Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe Afrika
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa Afrika
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Amince Da Naɗin Manyan Sakatarori 19 Afrika

Gwamnatin Gombe: Babu Hannun mu a Cin Zarafin Kansilan Mazabar Shamaki
Published: December 20, 2025 at 9:45 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Gombe ta musanta zargin da ƙungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International ta yi cewa, ana cin zarafi ko wulaƙanta waɗanda suka soki gwamnatin jahar.

Wata sanarwar da kakakin gwamnatin jahar Ismaila Uba Misilli ya fitar da yammacin Juma’a, ta ce babu ƙamshin gaskiya a zargin da ƙungiyar ta yi bayan wani faifan bidiyo ya nuna ɗaya daga cikin hadiman gwamnan jihar yana marin Kansilar gundumar Shamaki.

A sanarwar, Misilli ya ce bai kamata a riƙa alaƙanta lamarin da gwamnatin jihar ba, har ma ya yi gargaɗi game da saka siyasa kuma ya nesanta hannun wani jami’in gwamnati ko gwamnatin jhar a ciki.

Sanarwar ta ce babu wanda ya fi ƙarfin doka, kuma tuni aka fara ɗaukar matakan bincike dan ɗaukar mataki kan lamarin da ya sha suka daga al’umma.

Sanarwar ta kuma yi gargadin cewa a guji alaƙanta lamarin da gwamna ko gwamnatin jihar, tana mai cewa Gwamna Inuwa Yahaya baya goyon saɓa doka ko cin mutuncin wani.

A yanzu dai ƙungiyoyin da al’umma na jiran ganin matakin da gwamnatin za ta ɗauka a kan wanda ake zargin.

Siyasa

Post navigation

Previous Post: Matatar Man Dangote Ta Samu Tagomashi Daga Abokan Hulda
Next Post: Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi

Karin Labarai Masu Alaka

Dan Gudun Hijira Tarique Rahman Ya Kusa Zama Shugaban Kasa Labarai
APC Ta Yi Babban Taron Amincewa Da Shugabannin Jam’iyyar Ba Hamayya Afrika
Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
Jagoran Adawar Uganda Bobi Wine Ya Fice Daga Kasar Afrika
Gwamnatin Trump Tana Cigaba Da Korar Baki Daga Amurka Afrika
INEC: Akwai Yiwuwar Dage Zaben 2027 Saboda Azumi Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24
  • 3G Taskforce Ya Dasa Bishiyoyi Don Kare Muhalli A Gombe
  • Builder Mahmood Yusuf Ya Tallafa Wa Mata Da Matasa
  • Trump Ya Yi Gargadi Kan Shirin Cire Shugaban FIFA Infantino
  • Katsina United Ta Yi Jimamin Mutuwar Ɗan Wasanta Ozoh

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Samu Nasarar Karbo Karin Yara 130 Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Iran Ta Kama Wani Jirgin Ruwa Shake Da Mai Labarai
  • Za’a Jima Ana Fama Da Tsadar Farashin Mai Afrika
  • Sarkin Gombe Yayin Hawan Tudun Wada Labarai
  • Iran Da Amurka Zasu Cimma Yarjejeniyar Nukiliya Amurka
  • NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa Amurka
  • Gwannatin Jihar Kebbi Ta Arawa Maniyyata Kuɗin Aikin Hajji 2026, Labarai
  • Kasar Kenya Zata Samar Da Makamashi Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.