Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Ko Meye Gaskiyar Rade-Radin Zanga-Zanga A Jos Dake Jihar Filato
Published: March 6, 2026 at 1:08 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wani sako cikin murya da ke yawo a kafafen sada zumunta na zamani ya tada hankalin mazauna garin Jos da kewaye.
Mai maganar, a cikin dakika talatin da takwas an jiyo shi yana shaida wa wani cewa kada ya fito daga gidanshi saboda za’a yi zanga-zanga a Jos.
Muryar da ta karade shafukan sada zumunta ta sanya fargaba a zukatan mutane da waswasin hana ‘ya’yansu zuwa makaranta da fita kasuwanci.
Kan haka ne kwamishinan ‘yan sanda na jihar Filato, Bassey Ewah ya kira taron gaggawa da matasan kungiyar Islamic Movement of Nigeria wato kungiyar Shi’a don jin karin bayani kan ko suna shirin yin tattaki ne, ganin yadda ya gudana a wassu jihohin Najeriya, biyo bayan yakin dake aukuwa tsakanin kasar Amurka da Isra’ila da Iran.
Adam Khalid Muhammad shine wakilin dalibai na kungiyar ‘yan’uwa Musulmi a Najeriya, reshen jihar Filato, dake karkashin jagorancin Sheikh Ibrahim El-zakzaki yace sun shaida wa komishinan ‘yan sandan cewa basu san inda maganar zanga-zanga ta bullo ba.
Shima jagorar kungiyar a Jihar Filato, Sheikh Muhammad Auwal Abubakar yace kungiyarsu tana da tsari na mutunta ‘yancin kowa, don haka basu da niyyar tozarci ko kuntata wa kowa.
Rundunar ‘yan sandan ta jihar Filato dai ta kara tsaurara matakan tsaro a cikin garin Jos, musamman a unguwannin da take kira Flash Points, wato wuraren da ke da barazanar barkewar rikici, ciki har da kasuwanni.
Wakiyar Amurka Ke Magana a Jos Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton
https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/03/RADE-RADIN-ZANGA-ZANGA-A-JOS.mp3
Labarai

Post navigation

Previous Post: Jirgin Dakon Iskar Gas Daga Rasha Ya Sake Hanya
Next Post: Shugaban Najeriya Tinubu Ya Amince Na Tura Jakadu

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar China Tana Cigaba Da Nuna Fin Karfi Ga Kasar Taiwan Labarai
An Bukaci Sabbin Shugabanni Su Yi Jagoranci Nagari da Inganta Ayyukan Jama’a Labarai
Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai
‘Yan Tawayen Houthi Sunkai Hari Isra’ila Afrika
Baitul Malin Amurka Zata Bawa Venezuela Da Cuba Damar Sayar Da Mai Amurka
SERVICOM, ATBUTH Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Damfara Ne Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Laraba 11.19.2025 Rediyo
  • Majalisar Tarayya Ta Amince Da Mutane Uku A Matsayin Jakadun Kasashen Waje Labarai
  • Gwamnatin Najeriya Ta Tallafa Wa ’Yan Sanda Da Motoci Afrika
  • NAHCON Ta Yaba da Nasarar Hajjin 2026, Ta Fara Shirin Hajjin Shekara Mai Zuwa Amurka
  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe Afrika
  • Bahagon Mancha Ya Buge Bahagon Maitakwasara Da Wasun Su! Nishadi
  • Ana Cigaba Da Jimamin Rasuwar Mataimakin Gwamnan Bayelsa Najeriya
  • Gwamnatin Jihar Filato Ta Sauke Hakimin Mushere Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.