Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Ko Meye Gaskiyar Rade-Radin Zanga-Zanga A Jos Dake Jihar Filato
Published: March 6, 2026 at 1:08 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wani sako cikin murya da ke yawo a kafafen sada zumunta na zamani ya tada hankalin mazauna garin Jos da kewaye.
Mai maganar, a cikin dakika talatin da takwas an jiyo shi yana shaida wa wani cewa kada ya fito daga gidanshi saboda za’a yi zanga-zanga a Jos.
Muryar da ta karade shafukan sada zumunta ta sanya fargaba a zukatan mutane da waswasin hana ‘ya’yansu zuwa makaranta da fita kasuwanci.
Kan haka ne kwamishinan ‘yan sanda na jihar Filato, Bassey Ewah ya kira taron gaggawa da matasan kungiyar Islamic Movement of Nigeria wato kungiyar Shi’a don jin karin bayani kan ko suna shirin yin tattaki ne, ganin yadda ya gudana a wassu jihohin Najeriya, biyo bayan yakin dake aukuwa tsakanin kasar Amurka da Isra’ila da Iran.
Adam Khalid Muhammad shine wakilin dalibai na kungiyar ‘yan’uwa Musulmi a Najeriya, reshen jihar Filato, dake karkashin jagorancin Sheikh Ibrahim El-zakzaki yace sun shaida wa komishinan ‘yan sandan cewa basu san inda maganar zanga-zanga ta bullo ba.
Shima jagorar kungiyar a Jihar Filato, Sheikh Muhammad Auwal Abubakar yace kungiyarsu tana da tsari na mutunta ‘yancin kowa, don haka basu da niyyar tozarci ko kuntata wa kowa.
Rundunar ‘yan sandan ta jihar Filato dai ta kara tsaurara matakan tsaro a cikin garin Jos, musamman a unguwannin da take kira Flash Points, wato wuraren da ke da barazanar barkewar rikici, ciki har da kasuwanni.
Wakiyar Amurka Ke Magana a Jos Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton
https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/03/RADE-RADIN-ZANGA-ZANGA-A-JOS.mp3
Labarai

Post navigation

Previous Post: Jirgin Dakon Iskar Gas Daga Rasha Ya Sake Hanya
Next Post: Shugaban Najeriya Tinubu Ya Amince Na Tura Jakadu

Karin Labarai Masu Alaka

Malami: Gwamnatin APC Ta Gaza – “Yan-Kasa Kuwa Na Da Katin Zabe” Labarai
Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi Afrika
Wasu Mayakan ‘Yan Tawaye Sunkai Hari Filin Jirgin Saman Kasar Kwango Labarai
Limamin Da Ya Ceci Kiristoci Lokacin Rikicin Addini A Jihar Filato Ya Rasu Labarai
Gwamnatin Kano Ta Rufe Gidajen Bukukuwa Da Shakatawa Labarai
Shugaba Tinubu: Naji Dadin Sako Daliban Neja Da Aka Sace Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz
  • Shugaba Tinubu Yasa Hannu Kan Dokar Kasafin 2026
  • Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba
  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Zargi Babban Mai Gabatar Da Kara A Kotun Duniya Ta ICC Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Horar Da Matasa Sama 7,000 A Matsayin Masu Tsaron Daji Labarai
  • Amurka Zatayi Amfani Da Sansanonin Birtaniya Amurka
  • Kasar Colombia Tare Da Amurka Zasu Fitar Da Man Venezuela Labarai
  • Gwamna Abba Gida-Gida Na Dari-Darin Shiga APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kauran Gwandu Zai Inganta Wutan Lantarki A Kebbi Siyasa
  • Ko Arsenal Zata Iya Lashe Gasar Firimiya lig Na Bana Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Yayi Magana Game Da Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.