Wani sako cikin murya da ke yawo a kafafen sada zumunta na zamani ya tada hankalin mazauna garin Jos da kewaye.
Mai maganar, a cikin dakika talatin da takwas an jiyo shi yana shaida wa wani cewa kada ya fito daga gidanshi saboda za’a yi zanga-zanga a Jos.

Muryar da ta karade shafukan sada zumunta ta sanya fargaba a zukatan mutane da waswasin hana ‘ya’yansu zuwa makaranta da fita kasuwanci.
Kan haka ne kwamishinan ‘yan sanda na jihar Filato, Bassey Ewah ya kira taron gaggawa da matasan kungiyar Islamic Movement of Nigeria wato kungiyar Shi’a don jin karin bayani kan ko suna shirin yin tattaki ne, ganin yadda ya gudana a wassu jihohin Najeriya, biyo bayan yakin dake aukuwa tsakanin kasar Amurka da Isra’ila da Iran.
Adam Khalid Muhammad shine wakilin dalibai na kungiyar ‘yan’uwa Musulmi a Najeriya, reshen jihar Filato, dake karkashin jagorancin Sheikh Ibrahim El-zakzaki yace sun shaida wa komishinan ‘yan sandan cewa basu san inda maganar zanga-zanga ta bullo ba.
Shima jagorar kungiyar a Jihar Filato, Sheikh Muhammad Auwal Abubakar yace kungiyarsu tana da tsari na mutunta ‘yancin kowa, don haka basu da niyyar tozarci ko kuntata wa kowa.
Rundunar ‘yan sandan ta jihar Filato dai ta kara tsaurara matakan tsaro a cikin garin Jos, musamman a unguwannin da take kira Flash Points, wato wuraren da ke da barazanar barkewar rikici, ciki har da kasuwanni.
Wakiyar Amurka Ke Magana a Jos Zainab Babaji tana dauke da cikekken rahoton


