Ranar litinin, Britaniya tayi kira ga Isra’ila ta janye shawarar da ta yanke na fadada iko a yammacin kogin Jordan, furuci da ya saka ta cikin jerin kasashen Saudiyya da hadaddiyar daular larabawa wajen sukar matakin na Israila.
“Britaniya da kakkausr lafazi ta soki shawarar da majalisar tsaron Israila ta yanke ranar Lahadi na fadada ikonta a yammcin kogin jordan,” inji gwamnatin kasar Britaniya. Masu sukar lamiri suka ce matakin na Israila tamkar kwace filaye ko muhallan da ta mamaye ne.
“Duk wani yunkuri na yin gaban kai wajen sake taswira ko yanayin al’umma Falasdinawa, abu ne baki daya da ba za’a lamunta dashi ba, kuma ya kaucewa dokokin kasa da kasa. Muna kiran Isra’ila ta janye wannan shawara nan take, gwamnatin Brtaniyan ta fada.
Ahalinda ake ciki kuma, sojojin Isra’ilan sun kashe mayakan sakai hudu a Rafah dake kudancin zirin Gaza ranar Litinin, bayanda suka fito daga hanyoyin da suke karkashin kasa, suka budewa sojojin wuta, kamar yadda dakarun na Israila suka fada.


