Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

An Kai Hari Da Jirgi Mara Matuki A Kusa Da Matatar Mai Din Kasar Sundan
Published: December 11, 2025 at 9:36 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

An kashe wasu mutane da dama a harin da aka kai da maraicen talata da jirgin saman drone a kusa da matatar mai mafi girma a kasar Sudan.

Rundunar sojojin wucin gadi ta RSF, wadda tun shekarar 2023 take gwabza yaki da rundunar sojojin kasar ta Sudan, ta ce sojojin gwamnati ne suka kai hari kan matatar dake Heglig, kwana guda a bayan da dakarun RSF suka kwace wannan matata dake kusa da bakin iyakar kasar da Sudan ta Kudu.

Dukkan sassan biyu sun fada ma kamfanin dillancin labarai na Associated Press cewa ba su da cikakken adadin wadanda aka kashe ko aka ji ma rauni, amma kafofin labarai a yankin sun ce an kashe shugabanni 7 na wasu kabilu tare da sojojin rundunar RSF

Rundunar RSF ta kuma ce akwai sojojin Sudan ta Kudu a wannan harin da ta ce ya saba dokoki na kasa da kasa.

Rundunar sojojin Sudan ta tabbatar da kai hari da jiragen drone wadanda ta ce an auna su ne a kan mayakan rundunar RSF.

Gwamnatin jihar Unity ta Sudan ta Kudu ta tabbatar da kashe sojoji uku na Sudan ta Kudu.

Afrika

Post navigation

Previous Post: NNPC Da Wasu Kamfanoni Sunyi Yarjejeniyar Iskar Gas
Next Post: Kasar Iceland Ta Kauracewa Bikin Gasar Wakokin Shekara Mai Zuwa

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumar Upper Benue Zata Inganta Noma A Dadinkowa Afrika
Majalisar Kwararrun Iran Ta Sanar Da Sabon Shugaban Addini Afrika
Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Harin Jos Afrika
APC Ta Yi Babban Taron Amincewa Da Shugabannin Jam’iyyar Ba Hamayya Afrika
Makiyaya Sun Shiga Matsala Sakamakon Fari A Kasar Kenya Afrika
Ministan Harkokin Wajen Najeriya Yayi Murabus Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Majalisar Wakilai Ta Rikon Kwaryar Nijar Ta Gudanar Da Zama Karo Na Biyu Afrika
  • Kungiyar ISIS Ta Dauki Alhakin Harin Kasar Nijar Afrika
  • Amurka Ta Kakaba Takunkumi Ga Kwamandojin Yakin Kasar Sudan Sauran Duniya
  • Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
  • An Damke Wani Likita Da Ke Taimakawa ‘Yan-Ta’adda Najeriya
  • Kudaden Shigan Kasar Namibia Ya Bunkasa Saboda Tashin Farashin Gwal Labarai
  • Talauci Ya Ragu A Tsakanin Al’ummar Jihar Jigawa Siyasa
  • Shugabar Kungiyar Cinikayya Ta Duniya Ta Bukaci Kasashe Su Gyara Harkokin Cinikayya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.