Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Gobara Mafi Muni Cikin Shekaru 60 A Hong Kong Ta Hallaka Rayuka
Published: November 27, 2025 at 7:12 PM | By: Nafisa Ahmad

Wutar gobara mafi muni da aka gani a Hong Kong cikin shekaru fiye da 60, ta kwana tana ci, inda ya zuwa yanzu an ce akalla mutane arbain da hudu (44) ne suka mutu, yayin da ba a san inda wasu dari biyu da saba’in da tara (279) suke ba.

Har yanzu dai jami’an agaji suna ci gaba da zakulo mutane daga benayen da har zuwa safiyar nan suna ci da wuta.

‘Yan sanda sun kama mutane uku bisa zargin haddasa mutuwa dangane da wannan wuta da ta fara tashi tun jiya laraba da tsakar rana. Ya zuwa safiyar yau Alhamis agogon Hong Kong, ba a iya kashe wutar baki daya ba.

Jami’ai sun ce arba’in (40) daga cikin mutanen sun mutu a wurin ne, sauran hudu (4) kuma a asibiti. Wasu mutanen su akalla sittin da biyu (62) sun samu raunuka, wasu kunar wuta, wasu kuma shakar hayaki.

Mutanen da aka kama suna da alaka da kamfanin kwangila da ya gina benayen, inda ake tsammanin an yi amfani da wasu kayayyakin da ba su iya jure ma wuta, abinda ya saba doka.

Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Allah Ya Yi Wa Sheikh Dahiru Bauchi Rasuwa
Next Post: Wani Dan Bindiga Ya Harbi Dakarun Tsaron Cikin Gida Su Biyu A Washington DC

Karin Labarai Masu Alaka

Ranar Talata Amurka Da Isra’ila Sun Cigaban Da Kai Farmaki Iran Afrika
Alhinin Rasuwar Bello Sharada, Fitaccen Mai Sharhi Kan Siyasar Najeriya Afrika
Tinubu Ya Taya Shettima Murnar Cika Shekaru 60, Ya Yabi Gudunmawarsa Ga Najeriya Afrika
Akwai Yiwuwar Farashin Mai Zai Kara Tashi Afrika
NANPAN Ta Wayar Da Al’umma Kan Amfanin Shayar Da Jarirai Nono Kaɗai Afrika
Iran Zata Mayarwa Amurka Martanin Harin Kharg Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Za’a Ninka Shekarun Kurkuku Ga Masu Aikata Luwadi A Senegal Afrika
  • Zabebben Shugaban Hungary Yace Zaidawo Da Tsarin Dimokraɗiyya Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Masu Zuba Jari A Birnin Paris Afrika
  • Majalisa Ta Tabbatar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan Kano Afrika
  • Gwamnatin Amurka Da Najeriya Sunyi Hadakar Inganta Asibiticin Kiristoci Amurka
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
  • Tinubu Yafara Wasu Dabaru Domin Samun Kuri’u Siyasa
  • Asusun IMF Zasu Ziyarci Kasar Gabon Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.