Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika

Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Kudurin Kasar Ghana
Published: March 27, 2026 at 7:50 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Majalisar Dinkin Duniya ta amince da kudurin da kasar Ghana ta gabatar a ranar Laraba na ta yarda da bautar da mutane a ketaren tekun Atlantika a matsayin laifi mafi muni ga dan Adam, kuma an yarda da kudurin neman diyya, duk da bijirewa da aka samu daga Turai da kuma Amurka.

Ghana tace ana bukatar wannan kuduri, saboda abunda bautar da mutane ya haddasa, inda aka dauki a kalla mutanen Afrika miliyan 12 da dubu 500, aka sayar da su tsakanin karni na 15 zuwa karni na 19, har yau ana fuskantar sa, ciki har da wariyar launin fata.

A kuri’ar da aka kada a babban taro na Majalisar Dinkin Duniya, kasashe 123 sun goyi bayan kudurin, uku kuma basu goyi baya ba, cikin su akwai Amurka da Isra’ila, sannan kasashe 52 basu kada kuri’a ba, ciki da Tarayya Turai da Birtaniya.

Justin Howard, Ferfesa a Fannin Shari’a a jami’ar Howard yace kudurin nada muhimmanci, saboda yana nuni da matakin koli da Majalisar Dinkin Duniya ta dauka wajen amincewa da bautar da mutane a ketaren tekun Atlantika a matsayin cin zarafin dan adam, da kuma kira da a biya diyya.

Sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya shaidawa babban taron Majalisar cewa ana bukatar sauran kasashe su dauki mataki don fuskantar rashin adalcin da aka tafka a baya. Kasar Netherlands har yanzu ita ce kasa daya tilo a Turai da ta bayar da hakuri kan rawar da ta taka a bautar da mutane.

Afrika, Labarai, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Isra’ila Ta Cire Sunayen Wasu Mutane Biyu Cikin Wadanda Take Fako
Next Post: Shugaban Hukumar Kwallon Kafa Ta Senegal Yaki Amincewa Da Hukuncin CFA

Karin Labarai Masu Alaka

Rashin Kyawun Hanyoyi Babbar Matsalace A Najeriya Afrika
Malaman Addinin Musulunci Da Kirista Sunyi Bikin Cika Shekara 15 Na Iftar A Najeriya Afrika
An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango Afrika
An Gudanar Da Addu’o’i Na Musamman Don Neman Zaman Lafiya Labarai
Matatar Man Dangote Ta Kara Yawan Mai Dake Zuwa Kasashen Afirka Afrika
Gwamnan Jihar Filato Ya Karbi Katin APC Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ukraine Ta Aika Tawagar Kwararru Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine Labarai
  • Gwamnatin Amurka Tana Ganawa Da Manyan Jami’an Leken Asiri Amurka
  • Kimanin Ganga Miliyan 40 Na Danyen Albarkatun Mai Yayi Kwantai A Kasashen Afirka Ta Yamma Afrika
  • Abba Kabir: Zamu Samar da Jirage Marasa Matuka A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Canada Ta Amince A Shigar Da Motoci Kirar Kasar China Kasar Amurka
  • Jam’iyyar ADC Ta Karbi Peter Obi Da Wasu Manyan ‘Yan-Siyasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Kai Hari Kan Masu Hakar Ma’adanai A Kasar Mali Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.