Majalisar Dinkin Duniya ta amince da kudurin da kasar Ghana ta gabatar a ranar Laraba na ta yarda da bautar da mutane a ketaren tekun Atlantika a matsayin laifi mafi muni ga dan Adam, kuma an yarda da kudurin neman diyya, duk da bijirewa da aka samu daga Turai da kuma Amurka.
Ghana tace ana bukatar wannan kuduri, saboda abunda bautar da mutane ya haddasa, inda aka dauki a kalla mutanen Afrika miliyan 12 da dubu 500, aka sayar da su tsakanin karni na 15 zuwa karni na 19, har yau ana fuskantar sa, ciki har da wariyar launin fata.
A kuri’ar da aka kada a babban taro na Majalisar Dinkin Duniya, kasashe 123 sun goyi bayan kudurin, uku kuma basu goyi baya ba, cikin su akwai Amurka da Isra’ila, sannan kasashe 52 basu kada kuri’a ba, ciki da Tarayya Turai da Birtaniya.
Justin Howard, Ferfesa a Fannin Shari’a a jami’ar Howard yace kudurin nada muhimmanci, saboda yana nuni da matakin koli da Majalisar Dinkin Duniya ta dauka wajen amincewa da bautar da mutane a ketaren tekun Atlantika a matsayin cin zarafin dan adam, da kuma kira da a biya diyya.
Sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya shaidawa babban taron Majalisar cewa ana bukatar sauran kasashe su dauki mataki don fuskantar rashin adalcin da aka tafka a baya. Kasar Netherlands har yanzu ita ce kasa daya tilo a Turai da ta bayar da hakuri kan rawar da ta taka a bautar da mutane.


