Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutun Sallar Azumi
Published: March 17, 2026 at 4:14 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ayyana ranakun Alhamis 19 ga Maris da Juma’a 20 ga Maris, 2026 a matsayin ranakun hutun ƙasa domin bikin Ƙaramar Sallah (Eid-ul-Fitr).

Sanarwar ta fito ne ta bakin Babbar Sakatare a Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida, Magdalene Ajani, wadda ta ce Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayar da umarnin ayyana hutun a madadin Gwamnatin Tarayya.

Ministan ya taya al’ummar Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan, inda ya buƙace su da su ci gaba da riƙe kyawawan ɗabi’u da suka koyu a lokacin azumin, ciki har da soyayya, karamci, haƙuri da sadaukarwa.

Haka kuma, ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su yi amfani da wannan lokaci na bukukuwa wajen yi wa ƙasa addu’o’in zaman lafiya, haɗin kai da cigaba mai ɗorewa.

Tunji-Ojo ya kuma yi kira ga jama’a da su gudanar da shagulgulan Sallah cikin natsuwa tare da miƙa hannu ga marasa galihu, domin su ma su more farin cikin wannan lokaci na ibada.

Afrika, Labarai, Najeriya, Nishadi

Post navigation

Previous Post: Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
Next Post: An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Rasha Ta Zargi Ukraine Da Kai Hari Gidan Shugaban Rasha Amurka
An Gano Wasu Boma Bomai Da Aka Binne A Jihar Neja Najeriya
‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara Afrika
Isra’ila Zata Kai Hari Cibiyar Makamashin Iran Afrika
Gwamnatin Gombe Ta Kulla Yarjejeniyar Da New Zealand Kimiya
Rahoton Leken Asiri Yanuna Cewa Harin Amurka Bazai Samar Da Shugabanci A Iran Ba Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz
  • Shugaba Tinubu Yasa Hannu Kan Dokar Kasafin 2026
  • Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba
  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zabebben Shugaban Hungary Yace Zaidawo Da Tsarin Dimokraɗiyya Afrika
  • Shirin Manuniya Yau Juma’a 12.12.2026 Shirye-Shirye
  • Fadar Shugaban Ƙasan Najeriya Ta Musanta Wani Labarin ƙarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Borno Tsaro
  • Majalisar Dattawa Ta Wanke Janar Christopher Musa A Matsayin Minista Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Najeriya Tinubu Ya Amince Na Tura Jakadu Labarai
  • Kasar Belarus Zata Taffawa Jamhuriyar Nijar Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.