Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutun Sallar Azumi
Published: March 17, 2026 at 4:14 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ayyana ranakun Alhamis 19 ga Maris da Juma’a 20 ga Maris, 2026 a matsayin ranakun hutun ƙasa domin bikin Ƙaramar Sallah (Eid-ul-Fitr).

Sanarwar ta fito ne ta bakin Babbar Sakatare a Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida, Magdalene Ajani, wadda ta ce Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayar da umarnin ayyana hutun a madadin Gwamnatin Tarayya.

Ministan ya taya al’ummar Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan, inda ya buƙace su da su ci gaba da riƙe kyawawan ɗabi’u da suka koyu a lokacin azumin, ciki har da soyayya, karamci, haƙuri da sadaukarwa.

Haka kuma, ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su yi amfani da wannan lokaci na bukukuwa wajen yi wa ƙasa addu’o’in zaman lafiya, haɗin kai da cigaba mai ɗorewa.

Tunji-Ojo ya kuma yi kira ga jama’a da su gudanar da shagulgulan Sallah cikin natsuwa tare da miƙa hannu ga marasa galihu, domin su ma su more farin cikin wannan lokaci na ibada.

Afrika, Labarai, Najeriya, Nishadi

Post navigation

Previous Post: Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
Next Post: An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko

Karin Labarai Masu Alaka

Za’a Jima Ana Fama Da Tsadar Farashin Mai Afrika
Mutane Biyu Sun Mutu A Yayin Zaben Shugabannin Gundumomin APC A Jihar Ondo Najeriya
Kungiyar ECOWAS Ta Koka Game Da Yawan Juyin Mulki A Kasashen Afirka Afrika
Mataimakin Shugaban Kasar Amurka Ya Gana Da Wasu Wakilai Amurka
Rasha Da Ukraine Sun Cigaba Da Yakar Juna Afrika
‘Yan Bindiga A Mali Sun Kashe Direbobin Manyan Motoci Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jami’an Tsaro Na Amfani Da Damar Su Wajen Cin Zarafin Jama’a Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zanga-Zangar Adawa Da Harin Amurka Da Isra’ila Ya Zamo Tarzoma A Pakistani Afrika
  • Shugabar Hamayya A Venezuela Ta Gana Da Paparoma Leo Amurka
  • An Katse Intanet Da Wayar Tarho A Kasar Uganda Siyasa
  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe Afrika
  • Duniyar Dambe A Makon Jiya Nishadi
  • Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati Labarai
  • Za’a Saka Tarihin Trump A Manhajar Makarantu Don Jajircewasa Da Kwazo Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.