Ranar Alhamis shugaban Amurka Donald Trump yayi barazanar tura sojoji jahar Minnesota, karkashin wata dokar kasa data bashi ikon yin haka, bayan da aka kwashe kwanaki ana zazzafar zanga zanga kan tura karin jami’an shige da fice na kasar ko Immgiration kan titunan birnin Minneaplis.
Arangama ta tsananta tsakanin mazauna birnin da jami’an gwamnatin Amurka, bayan da wani jami’in hukumar Custom ya harpe tare kashe wata ba Amurkiya mai suna Renee Good a ckin motarta kwanaki takwas da suka wuce a birnin na Minneapolis, yanzu zanga zangar tana ba zuwa wasu birane.
Barazanar da shugaba Trump yayi a baya bayan nan, tana zuwa ne sa’o’i kacal, bayan da wani jami’in shige da fice ya harbi wani dan kasar Venezueala, wanda gwamnati tace ya gudu bayanda jami’ai suka yi kokarin tsaida motarsa a birnin ma Minneapolis.
Trump, wanda dan jam’iyyar Republican ne ya dauki makonni yana sukar lamirin shugabannin jam’iyyar Democrat a jahar Minnesota, ya kira al’umar Somali a jahar a zaman “shara ko dotti, wadanda a cewarsa “tilas a kore su daga cikin kasan nan.”
Ahalin da da ake ciki kuma, kuri’ar neman jin ra’ayin jama’a ta nuna ‘yan jam’iyyar Republican sun kasu gida biyu, kan yadda suke kallon matakan yaki da bakin haure da gwamnatin shugaba Trump ta sa agaba.


