Gwamnatin Tarayya ta cire sharadin rubuta jarabawar shiga manyan makarantu ta UTME ga daliban da ke neman shiga Kwalejojin Ilimi na ƙasa.
Ministan Ilimi na Najeriya, Tunji Alausa ne ya bayyana hakan a matsayin wani mataki na ƙarfafa ɗalibai su shiga karatun horas da malamai a faɗin ƙasar.
Sabon tsarin ya nuna cewa masu neman gurbin karatu a Kwalejojin Ilimi ba sai sun rubuta jarabawar UTME da Hukumar Joint Admissions and Matriculation Board ke gudanarwa ba kafin samun gurbin karatu.
An ce matakin na daga cikin ƙoƙarin gwamnati na magance ƙarancin masu neman shiga Kwalejojin Ilimi tare da ƙara yawan ƙwararrun malamai a fannin ilimi a Najeriya.
Masu ruwa da tsaki a harkar ilimi na ganin cewa wannan mataki zai taimaka wajen faɗaɗa damar shiga karatun koyarwa da kuma rage ƙarancin malamai a makarantu.


